Firai ministan kasar Habasha Abiy Ahmed ya bukaci kungiyar tarayyar Afirka AU ta bunkasa aikin cibiyar yaki da cututtuka na kungiyar wato CDC don biyan bukatun kiwon lafiya na kasashen nahiyar gaba daya.

Kamfanin dillancin labaran Sputnic na kasar Rasha ya nakalto Abiy Ahmed yana fadar haka a lokacinda yake ganawa da daraktan hukumar ta CDC a birnin Adis Ababa a ranar Jumma’an da ta gabata.

An kafa cibiyar yaki da cututtuka ta kungiyar tarayyar Afirka (CDC) ne, a shekara 2016, sannan ta fara aiki a shekara ta 2017 don kawo ci gaba a harkokin kiwon lafiyar a nahiyar Afirka.

Gwamnatin kasar China ce ta taimaka aka gina gine-gine cibiyar, aka kuma fara amfani da su a shekara ta 2023.

Abiy yace bunkasa cibiyar ta CDC zai taimakawa kasashen Afirka magance matsalolin kiwon lafiaya da dama a nahiyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dantsoho Ya Yaba Wa Ƙoƙarin Oyetola Na Dawo Da Nijeriya Tsarin Sufurin Jiragen Ruwa Na Duniya

“Dawo Nijeriya a cikin rukunin na C a kungiyar ta IMO hakan ya nuna irin zagewar kasar nan na iya tafiyar da tsare-tsare da bin ka’idojin gudanar da sufurin Jiragen Ruwa da wanzar da tsaro da kuma samar da kyakyawan yanayi, ga fannin,” Inji Dantsoho.

“Wannan ci gaban, ba wai ga kasar nan ne kadai ba, har da ma ci gaban daukacin Afirka ta Yamma musamman a bangaren kara bunkasa ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a nahiyar da samar da hanyoyin kara habaka safarar kaya zuwa ketare da kuma kara bunkasa fannin tattalin arziki na teku'” A cewar shugaban.

“Nijeriya a yau, ta kai wani babban mataki da duniya ke sauraronta a saboda haka, ina kara taya Nijeriya da hukumar ta NPA kan wannan nasarar da ta samu'” Inji Dantsoho.

Shugaban ya kuma yabawa ministan bunkasa tattalin arziki Dakta Adegboyega Oyetola, musamman kan jajircewarsa, wajen daga matsayin kasar nan, a fannin kula da lafiyar da sufurin Jiragen Ruwa na kasa

r nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi December 13, 2025 Manyan Labarai Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman December 13, 2025 Manyan Labarai Matatar Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699 December 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Eritrea Ta Fice Daga Kungiyar Raya Kasahsen Gabacin Afrika (IGAD)
  • َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja
  • Me Ke Kawo Yawaitar Juyin Mulki A Nahiyar Afirka?
  • DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
  • Kalibaf:  Iran Da Habasha Suna Bunkasa Alakokin Siyasa Da Tattalin Arziki
  • Dantsoho Ya Yaba Wa Ƙoƙarin Oyetola Na Dawo Da Nijeriya Tsarin Sufurin Jiragen Ruwa Na Duniya
  • Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan
  • Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa
  • Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026