Kasar Habasha Ta Bukaci Kasashen Afirka Su Bunkasa Ciyar Yaki Da Cututtuka CDC Da Kungiyar
Published: 17th, March 2025 GMT
Firai ministan kasar Habasha Abiy Ahmed ya bukaci kungiyar tarayyar Afirka AU ta bunkasa aikin cibiyar yaki da cututtuka na kungiyar wato CDC don biyan bukatun kiwon lafiya na kasashen nahiyar gaba daya.
Kamfanin dillancin labaran Sputnic na kasar Rasha ya nakalto Abiy Ahmed yana fadar haka a lokacinda yake ganawa da daraktan hukumar ta CDC a birnin Adis Ababa a ranar Jumma’an da ta gabata.
An kafa cibiyar yaki da cututtuka ta kungiyar tarayyar Afirka (CDC) ne, a shekara 2016, sannan ta fara aiki a shekara ta 2017 don kawo ci gaba a harkokin kiwon lafiyar a nahiyar Afirka.
Gwamnatin kasar China ce ta taimaka aka gina gine-gine cibiyar, aka kuma fara amfani da su a shekara ta 2023.
Abiy yace bunkasa cibiyar ta CDC zai taimakawa kasashen Afirka magance matsalolin kiwon lafiaya da dama a nahiyar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ta tabbatar da rasuwar wasu mutum biyar sakamakon haɗura uku da suka auku a jihar.
Kakakin hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ya ce hatsrin farko ya faru ne da safiyar ranar Alhamis a unguwar Badawa Layin Day by Day ca Ƙaramar Hukumar Nassarawa.
Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin Jirgin sojin sama ya yi hatsari a NejaLamarin ya faru ne a wani gida mai faɗin kafa 25 da 20 wanda ya kama da wuta.
Ma’aikatan kashe gobara sun ceto wata yarinya mai shekara 10 daga a cikin gidan, amma daga baya ta rasu a asibiti.
An bai wa iyayenta gawarta.
Hatsari na biyu ya faru ne a Ƙauyen Badume Kanawa da ke Karamar Hukumar Bichi.
Wani mutum mai shekara 65, Sa’idu Gada, yana aiki a cikin rijiya lokacin da igiyar da ta ke riƙe da shi ta tsinke, ya faɗa ciki.
Ɗansa mai shekara 20, Sani Isyaku, ya shiga rijiya domin ceto shi, shi ma ya maƙale.
Wani mutum na uku, Yakubu Abdullahi mai shekara 60, ya shiga domin taimakonsu, shi ma daga bisani ya faɗa cikin rijiyar.
Ma’aikatan hukumar sun fito da su daga rijiyar, amma sun riga sun rasu.
An miƙa wa ’yan sandan Badume gawarwakinsu.
A wani lamari na daban kuma, wani yaro mai shekara 10, Hassan Iliyasu Haruna, ya zame tare da faɗa wa rijiya a Ƙaramar Hukumar Danbatta.
Ma’aikatan hukumar kashe gobara sun ceto shi, amma daga baya ya rasu.
An miƙa wa mahaifinsa gawar yaron.
Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Kano, Sani Anas, ya ja hankalin jama’a da su daina shiga rijiya domin ceto mutane, domin a cewarsa hakan na da hatsari.