Firai ministan kasar Habasha Abiy Ahmed ya bukaci kungiyar tarayyar Afirka AU ta bunkasa aikin cibiyar yaki da cututtuka na kungiyar wato CDC don biyan bukatun kiwon lafiya na kasashen nahiyar gaba daya.

Kamfanin dillancin labaran Sputnic na kasar Rasha ya nakalto Abiy Ahmed yana fadar haka a lokacinda yake ganawa da daraktan hukumar ta CDC a birnin Adis Ababa a ranar Jumma’an da ta gabata.

An kafa cibiyar yaki da cututtuka ta kungiyar tarayyar Afirka (CDC) ne, a shekara 2016, sannan ta fara aiki a shekara ta 2017 don kawo ci gaba a harkokin kiwon lafiyar a nahiyar Afirka.

Gwamnatin kasar China ce ta taimaka aka gina gine-gine cibiyar, aka kuma fara amfani da su a shekara ta 2023.

Abiy yace bunkasa cibiyar ta CDC zai taimakawa kasashen Afirka magance matsalolin kiwon lafiaya da dama a nahiyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

A baya bayan nan, firaministan kasar Senegal Ousmane Sonko, ya zanta da kafar CMG ta kasar Sin, inda ya jinjinawa shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, wadda ya bayyana a matsayin mai cike da hangen nesa da burikan samar da ci gaba, wanda hakan ya yi daidai da hikima, da managarcin tunanin jagoranci na shugaba Xi Jinping na kasar Sin.

Mista Sonko, ya ce Senegal ce kasar farko a yammacin Afirka da ta karbi wannan shawara. Kuma abu ne mai muhimmanci ganin yadda shawarar ke kara ingiza cimma nasarori ga dukkanin sassan. Sonko ya kara da cewa, cikin ‘yan shekaru kalilan, tarin kasashen Afirka sun cimma manyan nasarori na hakika, daga aiwatar da shawarar.

Ya ce shawarar ba wai ta zo domin sauya alkiblar da daukacin kasashe ke bi ba ne, maimakon hakan, ta samar da zarafi ne na hadin gwiwa dake bayar da dama ga ko wace kasa, ta tattaunawa da Sin gwargwadon moriyar kashin kanta. Mista Sonko ya ce kasashen Afirka na da mabanbantan abubuwa da suke mayar da hankali kan su. Wasu na fatan bunkasa kayayyakin wasanni, wasu na da burin gina manyan hanyoyin mota, da masu fatan bunkasa masana’antu. Kuma Sin na tattaunawa da kasashe daban daban bisa la’akari da hakan, da fatan cimma kololuwar gajiya tare. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko
  • Hizbullah Ta Yi Allawadai Da Harin HKI A Kasar Yemen
  • Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yaba Da Kungiyar BRICS Saboda Yin Tir Da HKI A Yakin Kwanaki 12
  • Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
  • Iran ta Bukaci Gudanar da Bincike Kan Sacewar jami’ar Diblomasiyyar kasar A Lebanon Shekaru 43 Da Suka gabata
  • Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa
  • Kungiyar Hamas Ta Ce Ta Amince Da Tattaunawa Don Kawo Karshen Yaki A Gaza