Kasar Habasha Ta Bukaci Kasashen Afirka Su Bunkasa Ciyar Yaki Da Cututtuka CDC Da Kungiyar
Published: 17th, March 2025 GMT
Firai ministan kasar Habasha Abiy Ahmed ya bukaci kungiyar tarayyar Afirka AU ta bunkasa aikin cibiyar yaki da cututtuka na kungiyar wato CDC don biyan bukatun kiwon lafiya na kasashen nahiyar gaba daya.
Kamfanin dillancin labaran Sputnic na kasar Rasha ya nakalto Abiy Ahmed yana fadar haka a lokacinda yake ganawa da daraktan hukumar ta CDC a birnin Adis Ababa a ranar Jumma’an da ta gabata.
An kafa cibiyar yaki da cututtuka ta kungiyar tarayyar Afirka (CDC) ne, a shekara 2016, sannan ta fara aiki a shekara ta 2017 don kawo ci gaba a harkokin kiwon lafiyar a nahiyar Afirka.
Gwamnatin kasar China ce ta taimaka aka gina gine-gine cibiyar, aka kuma fara amfani da su a shekara ta 2023.
Abiy yace bunkasa cibiyar ta CDC zai taimakawa kasashen Afirka magance matsalolin kiwon lafiaya da dama a nahiyar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa
Babban magatakardar MDD Antonio Gutress ya yi suka da kakkausar murya akan kutsen da ‘yan sandan Haramtacciyar Isra’ila su ka yi a cikin cibiyar kungiyar Agaji ta “Unrwa” a gabashin birnin Kudus.
A bayanin da babban magatakardar MDD ya fitar ya ambaci cewa; Har yanzu ginin na “Unrwa” mallakin Majalisar Dinkin Duniya ne, yana da kariya da bai kamata a taba shi ko shiga cikinsa ba.
Haka nan kuma ya yi kira ga “Isra’ilan” da ta yi gaggauta dawo da hurumin ginin na MDD da ba shi kariya,sannan kuma da hana daukar wasu Karin matakai akan gine-ginen MDD.
A nashi gefen, shugaban hukumar Agajin ta “Unrwa” Phillipe Lazarani ya wallafa sako a shafinsa na X cewa; Abinda Isra’ilan ta yi, wani sabon kalubale ne ga dokokin kasa da kasa, ya kuma zama wajibi ta kare da girmama gine-ginen MDD.
A ranar Litinin din da ta gabata ne dai ‘yan sandan haramtacciyar kasar Isra’ila su ka kutsa cikin ginin hukumar agajin ta “Unrwa” a unguwar Jarrah, a gabashin birnin Kudus.
MDD ce dai ta kafa Unrwa ne a 1951 domin taimakawa al’ummar Falasdinawa, sai dai kuma HKI ta haramta kungiyar da haka ta gudanar da ayyukanta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu December 9, 2025 Faransa ta ce da hannunta aka dakile juyin mulki a Benin December 9, 2025 RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci