Leadership News Hausa:
2025-07-10@23:54:18 GMT

Ba Don Tarbiyantar Da Mutane Nake Yin Fim Ba -Amina Shehu Lulu

Published: 17th, March 2025 GMT

Ba Don Tarbiyantar Da Mutane Nake Yin Fim Ba -Amina Shehu Lulu

Da ta ke amsa tambaya a kan rayuwa kafin samun daukaka da kuma bayan samun daukaka, Lulu ta amsa da cewar akwai banbanci sosai a rayuwata ta baya da kuma yanzu, saboda yanzu mutane da dama sun sanni ba kamar kafin in fara harkar fim ba, a wancan lokacin mutane basu damu da kai ba amma yanzu kuma ka samu masoya da wadanda ke ganin ba daidai kake yin abubuwa ba, saboda haka dole ne abubuwa su canza sosai.

Daga karshe jarumar ta ce ba ta fatan ace ta shafe shekaru fiye da goma a masana’antar ta nishadi, don kuwa ba ta son ace sai ta tsufa sannan za ta daina harkar fim, ina fatan ganin nan da shekara goma ace na koma gefe na baiwa matasa masu tasowa wuri domin kuwa bani son ace sai na tsufa a masana’antar kafin a daina dora mani na’urar daukar hoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

A gabanin bikin cika shekaru 80 da kafuwar MDD, taron kwamitin kula da hakkin dan Adam na MDD wato UNHRC karo na 59 ya zartas da kudurin da kasar Sin ta gabatar dangane da muhimmancin ci gaba wajen kiyaye hakkin dan Adam. Wannan ne karo na farko da aka zartas da kudurin ta hanyar tattaunawa a maimakon kada kuri’a. Kasar Sin ta gabatar da kudurin ne a shekarar 2017.

Chen Xu, zaunannen wakilin kasar Sin a ofishin MDD dake Geneva da kungiyoyin kasa da kasa a kasar Switzerland ya yi karin bayani kan kudurin da cewa, kudurin ya sake nanata muhimmancin ci gaba wajen kiyaye hakkin dan Adam daga dukkan fannoni, tare da jaddada yadda ci gaba mai inganci kuma mai mayar da jama’a a gaban kome, yake taka muhimmiyar rawa kan kyautata jin dadin jama’a da kuma kara azama kan bunkasar hakkin dan Adam.

Har ila yau, kudurin da kasashe 42 ciki har da Kamaru da Pakistan suka gabatar cikin hadin gwiwa ya bayyana fatan kasashe masu tasowa. Wakilai daga kasashen Cuba, Bolivia, Habasha, Kenya sun bayyana cewa, kudurin zai kyautata kulawar da ake nunawa kan muhimmancin ci gaba wajen kiyaye hakkin dan Adam da kuma kara azama kan kiyaye hakkin dan Adam ta hanyar samun bunkasa mai dorewa. (Tasallah Yuan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  HKI Tana Cigaba Da Yi Wa Mutanen Gaza Kisan Kiyashi
  • An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
  • Har Yanzu A Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara
  • UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
  • Har Yanzu Cikin PDP Nake, Ba Zan Koma APC Ko ADC Ba – Gwamnan Zamfara
  • ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna Soludo
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja
  • HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya
  • Har Yanzu Ba A Ga Mutum 160 Bayan Ambaliyar Texas
  • ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027