Leadership News Hausa:
2025-12-10@15:27:17 GMT

Ba Don Tarbiyantar Da Mutane Nake Yin Fim Ba -Amina Shehu Lulu

Published: 17th, March 2025 GMT

Ba Don Tarbiyantar Da Mutane Nake Yin Fim Ba -Amina Shehu Lulu

Da ta ke amsa tambaya a kan rayuwa kafin samun daukaka da kuma bayan samun daukaka, Lulu ta amsa da cewar akwai banbanci sosai a rayuwata ta baya da kuma yanzu, saboda yanzu mutane da dama sun sanni ba kamar kafin in fara harkar fim ba, a wancan lokacin mutane basu damu da kai ba amma yanzu kuma ka samu masoya da wadanda ke ganin ba daidai kake yin abubuwa ba, saboda haka dole ne abubuwa su canza sosai.

Daga karshe jarumar ta ce ba ta fatan ace ta shafe shekaru fiye da goma a masana’antar ta nishadi, don kuwa ba ta son ace sai ta tsufa sannan za ta daina harkar fim, ina fatan ganin nan da shekara goma ace na koma gefe na baiwa matasa masu tasowa wuri domin kuwa bani son ace sai na tsufa a masana’antar kafin a daina dora mani na’urar daukar hoto.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja

An gano gawar wani malamin makarantar Islamiyya kuma mahaifin ’ya’ya bakwai, Malam Awwal Yakubu, a cikin wani kango da ke rukunin gidaje na Talba a birnin Minna, na Jihar Neja.

Malam Awwal, yana da makarantar Islamiyya a unguwar Barikin-Saleh, an neme shi sama ko ƙasa tun ranar Alhamis ɗin da ta gabata.

’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin

An gano gawarsa ne da safiyar ranar Lahadi.

Rahotanni sun nuna cewa an ƙone al’aurarsa, sannan an samu kwalin ashana a gefen gawarsa.

Shugaban al’ummar yankin, Malam Mahmud Dalhatu Iya, ya shaida wa Aminiya cewa iyalan mamacin sun riga sun gano gawar kuma an riga an binne shi.

Ya ce, “An sanar da ni cewa an ga wata gawa ta lalace a wani gini da ba a kammala ba a cikin rukunin gidajenmu.

“Mun kai wa ’yan sanda rahoto. Muna nan lokacin da wani ya zo ya ce shi abokin mamacin ne, ya kuma ya ɓace tun ranar Alhamis. An yi wa gawar sutura don yi mata jana’iza a lokacin da nake magana da ku.”

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce, “A yau, 7 ga watan Disamba 2025, da misalin ƙarfe 10 na safe, an samu rahoto cewa an ga gawa a bayan rukunin gidaje na Talba da ke kan titin Kpakungu.

“Jami’an ’yan sandan Kpakungu sun je wajen kuma sun gano gawar ta lalace cikin wani gini da ba a kammala ba.

“Daga bisani iyalansa suka tabbatar da cewa Auwal Yakubu ne, mai shekaru 45, mazaunin wannan yanki.”

Ya ƙara da cewa, “Ana zargin cewa an jefar gawar ne a wajen, domin an ruwaito ya ɓace tun a ranar 4 ga watan Disamba kafin a gano shi da safiyar yau.

“An kai gawar asibiti, kuma an fara bincike don gano musabbabin rasuwarsa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Kungiyar AU Ta yi Tir Da Harin Da RSF  Takai A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa