HausaTv:
2025-11-02@17:11:28 GMT

 Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa

Published: 5th, July 2025 GMT

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Kassim  ya mayar da martani ga wadanda suke son, kungiyar ta mika makamanta, yana mai cewa; Ku fara da neman makiya su fice daga cikin Lebanon, domin babu hankali ace ba ku cewa komai akan ‘yan mamaya,ya zamana kuna neman wanda yake gwgawarmaya ya ajiye makamansa.

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce: Duk wanda ya amince da mika wuya, ya yi, amma mu ba za mu laminta da hakan ba. Mu almajiran makarantar Imam Hussain ( a.s) ne da yake cewa: Ba Za Mu Taba Lamunta Da Kaskanci Ba.”

Sheikh Na’im Kassam ya ce: Wadanda suke jingina da kasashen waje, suna kuskuren lissafi, domin masu gwgawarmaya ba su ganin wani kwarjinin abokan gaba, ba kuma za su sarayar da hakkokinsu ba.”

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa: Babban ci gaba na hakika da aka samu shi ne ‘yanto da kasa, muna kuma cikin Shirin ci gaba da yin haka a kodayaushe.”

Sheikh Na’im Kassim ya jaddada cewa;raya lokacin shahadar Imam Hussain ( a.s),  raya musulunci ne da dukkanin bangarorinsa, da kuma manhajarsa.

 Haka nan kuma ya ce; Musulunci wanda Imam Hussian ( a,s) da iyalan gidansa su ka kare shi, shi ne fidirar mutum tabbatacciya, yana kuna ayyana nauyin da ya rataya akan kowance mutum daidai da gwargwadon dabi’arsa ta namiji ko mace. Nauyin da ya rataya a wuyan namiji shi ne daukar makami domin yin yaki na bayar da kariya, ita kuwa mace ba a dora mata yin hakan ba,amma a lokaci daya abokiyar tarayya ce a cikin jihadi ta hanyar rawar da take takawa a bayan fagen daga, da su ka hada yin tarbiyya da ayyukan da muhimmancinsu bai gaza na namiji a fagen daga ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Shugaba Bola Tinubu ya yi wa sabbin Shugabannin Sojoji ado da karin girma domin su dace da sabbin muƙamansu. Sabbin shugabannin rundunar sojin kasar da aka yi wa ado sun hada da Laftanar Janar, wanda yanzu ya zama Janar Olufemi Olatubosun Oluyede, a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS); da kuma Manjo Janar yanzu ya koma Laftanar Janar Emmanuel Undiendeye Undiendeye a matsayin Babban Hafsan Tsaro na farin kaya (CDI). Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  Sauran su ne Manjo Janar, wanda yanzu ya zama Laftanar Janar Waidi Shaibu a matsayin Babban Hafsan Soja (COAS); Air Vice Marshal, wanda yanzu ya zama Air Marshal Kevin Aneke a matsayin Babban Hafsan Sojan Sama; da kuma Rear Admiral, wanda yanzu ya zama Vice Admiral Idi Abbas a matsayin Babban Hafsan Sojan Ruwa. Shugaba Tinubu ya sanar da maye gurbin Shugabannin Rundunar tsaron ne a ranar Juma’ar da ta gabata, wani mataki da aka danganta da bukatar sake mai da hankali da kuma karfafa tsaron kasa. Bayan haka, Shugaba Tinubu ya bukaci sabbin Shugabannin Rundunar tsaron da su dauki mataki mai tsauri kan barazanar tsaro da ke tasowa a fadin kasar, yana mai gargadin cewa ‘yan Nijeriya na tsammanin ganin sakamako, ba uzuri ba. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai