An fara tuhumar tsohon ɗan ƙwallon Arsenal, Thomas Partey da laifuka biyar da suka haɗa da fyaɗe da kuma cin zarafi, an bayar da rahoton cewa ya aikata laifukan ne a tsakanin shekarar 2021-2022, cewar ‘yansandan Birtaniyya.

Daga cikin laifukan akwai fyaɗe akan wasu mata uku waɗanda ake tuhumarsa da cin zarafinsu ta hanyar tursasawa kan mace ta farko da ta biyu sai kuma laifin lalata da mace ta uku.

‘Yansanda a ƙasar Birtaniya sun ce ya kamata Thomas ya bayyana a Kotun Majistare ta Westminster a ranar 5 ga watan Agusta, tuhumar ta biyo bayan binciken da jami’an tsaro suka gudanar, wanda ya fara a watan Fabrairun 2022 bayan da ‘yansanda sun samu rahoton fyaɗen.

Partey dai ya bar Arsenal bayan kwantiraginsa ya ƙare, kuma an ce ƙungiyoyin da suka haɗa da Juventus da Barcelona da kuma Fenerbahce suna zawarcinsa, ɗan wasan na Ghana ya kasance a Emirates na tsawon shekaru biyar bayan an siyo shi daga Atletico Madrid, kuma ya buga wa ƙasarsa wasanni da dama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arsenal Zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Juyin mulki: Shugaba Rajeolina ya tsere daga ya rushe majalisa

Shugaban Madagascar, Andry Rajoelina, ya rusa majalisar dokoki ta ƙasar a yayin da rikicin soja ke ƙara ƙamari tare da neman hambarar da gwamnatinsa.

A ranar Talata ya sanar da rushe majalisar Dokoki ta Ƙasar, a daidai lokacin da ake fama da tarzomar soja da ta tilasta masa tserewa daga ƙasar.

A cewar wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta wallafa a shafinta na Facebook, Rajoelina ya fitar da wata doka da ke umartar rushe majalisar dokoki nan take.

Wannan mataki ya zo ne a daidai lokacin da wasu dakarun soja na musamman suka goyi bayan zanga-zangar matasa da ke neman sauya gwamnati, lamarin da ya haifar da ƙoƙarin juyin mulki.

Cirar kudin kwastoma: Majalisa ta gayyaci CBN da bankuna Gwamnan Enugu da kwamishinoninsa sun koma APC

Shugaban ya bayyana a wani jawabi da aka yaɗa ta kafafen sada zumunta a daren Litinin cewa ya fice daga ƙasar ne saboda tsoron rasa rayuwarsa.

Majalisar dokoki dai ta kasance cikin wani zama na musamman don tattauna yiwuwar tsige Rajoelina daga shugabancin ƙasa, amma rushewar da ya yi wa majalisar ya daƙile wannan yunƙuri gaba ɗaya.

Wannan doka da Rajoelina mai shekaru 51 ya fitar ta ƙara dagula siyasar Madagascar, mai yawan jama’a kimanin miliyan 31 a gabar tekun gabashin Afirka.

Tun wasu makonni da suka gabata, Rajoelina na fuskantar matsin lamba daga gungun matasa ’yan Gen Z da ke jagorantar zanga-zangar neman sauya gwamnati.

Aminiya ta fahimta cewa har yanzu ba a san inda shugaban ke ba, yayin da halin rashin tabbas ke ci gaba da mamaye al’amuran siyasa a ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 
  • Yadda Najeriya ta casa Jamhuriyar Benin 4-0
  • Ya kamata ‘yan fim su rika taimaka wa kananan cikinsu-Rukayya Abdullahi
  • Juyin mulki: Shugaba Rajeolina ya tsere daga ya rushe majalisa
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa
  • Sakin Maryam Sanda shi ne ƙololuwar zalunci —Dangin Bilyaminu
  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano