Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwon Gargajiya ta Afrika wato CORET, tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika ECOWAS, sun bayyana shirinsu na samar da ayyuka guda dubu uku ga matasa ta hanyar sarrafa madara a sarkar darajar madara a Jahohin Kaduna da Jigawa.

 

Shugaban Shirin na CORET, Dr.

Umar Hardo, ne ya bayyana hakan yayin taron horaswa da ƙungiyoyin haɗin kai Sha biyu da aka zaɓo wanda ya gudanar a yankin Ladduga dake ƙaramar hukumar Kachia a Jihar Kaduna.

Taron horaswar na tsawon kwanaki biyu ya haɗa shugabanni daga ƙungiyoyin kiwo na madara guda goma sha biyu, masu tara madara, da shugabannin al’umma. Wannan shiri da ECOWAS ta ɗauki nauyi, zai fara aiki gwaje ne a ƙauyuka biyu, a Ladduga a Jihar Kaduna da kuma Maigatari a Jihar Jigawa.

 

Haka kuma, an samu goyon baya daga Hukumar Ci gaban Kasar Sweden, inda ake aiwatar da aikin ta hanyar haɗin gwiwar wasu ƙungiyoyi kamar Hukumar Kula da Makiyaya da kuma da sauran su.

 

Dr. Umar Hardo ya bayyana cewa taron horaswar na nufin bai wa ƙungiyoyin haɗin kai horo da ilimi a duk fannoni na samar da madara domin cigabansu

 

“CORET ta riga ta shiga haɗin gwiwa da kamfanoni irin su Milk Copal, Nestlé da Farm Fresh. Kuma an gina cibiyoyin tarin madara masu amfani da hasken rana a Ladduga da Maigatari,” in ji shi.

 

Dr. Umar Hardo ya ƙara da cewa an tsara horaswar ne akan matasa dari huɗu, amma matasa dari tara da ashirin da uku daga Ladduga suka nuna sha’awar shiga, lamarin da ya nuna yadda matasa ke da sha’awar shiga ƙungiyoyin haɗin gwiwa.

Ya ce daga cikinsu, an zaɓi matasa dari huɗu daga Maigatari, Jihar Jigawa don samun horo a cikin shirin.

 

“CORET ta sanya hannu kan yarjejeniya da Ma’aikatar Noma ta Tarayya da kuma Ma’aikatun Noma na Jihohin Kaduna da Jigawa domin aiwatar da wannan aiki,” in ji shi.

 

Shugaban Shirin ya bayyana cewa wannan wani babban cigaba ne a tarihin Najeriya, domin wannan ne karon farko da ake gina cibiyoyin tara madara masu na’urorin sanyaya madara domin sauƙin jigilar ta ba tare da ta lalace ba.

 

Ya ƙara da cewa wani sashi na shirin, shi ne gina cibiyoyin tara madara tare da horas da mahalarta a matsayin masu tara madara daga karkara waɗanda za su kula da wadannan cibiyoyi da kuma ƙungiyoyin haɗin ksn.

 

A cikin Kasidarshi, Tsohon Darakta na Raya Al’umma da Ƙungiyoyin Haɗin Kai a Jihar Kaduna, Mista Yohanna Kabirat, ya ce horon ya mayar da hankali ne kan ƙungiyoyin haɗin Kai da gudanarwa, da shugabanci domin su gudanar da ƙungiyoyinsu cikin nasara.

 

Ya jaddada muhimmancin ƙungiyoyin haɗin kai wajen ci gaba mai ɗorewa ga membobinsu, musamman matasa na Ladduga.

 

Mista Kabirat ya shawarci mahalarta su isar da ilimin da suka samu ga sauran membobinsu, musamman wajen yin bayanawa kowa bayyanai ba tareda an boye ba wanda shi ne babban kalubalen da ya jefa ƙungiyoyi da dama cikin matsalolin kudi a baya.

 

Tsohon Daraktan a karshe yace tushen nasarar kowace ƙungiyar haɗin Kai shine bin dokokin ƙungiyar yadda ya kamata.

 

Da suke magana da Radio Nigeria Kaduna, wasu daga cikin mahalarta taron, Sufyanu Umar da Fatima Isa, sun bayyana farin cikinsu da horon da aka basu, inda suka ce sun samu ƙwarewa ta musamman wajen tafiyar da ƙungiyoyinsu cikin nasara da inganci.

 

Mahalarta taron horaswar sun yaba wa CORET da sauran abokan ci gaba bisa shirya taron horaswar da suka ce zai sauya rayuwarsu ta fannin samar da madara.

Sun bayyana cewa ilimin da suka samu zai kasance ginshiƙi mai ɗorewa ga rayuwarsu da ci gabansu.

 

Rahoto daga Adamu Yusuf.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ayyuka Jigawa Samarda

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Alhazai ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Maniyyatan Aikin Hajjin 2026 Su Fara Biyan Kudaden Ajiya

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna ta shawarci maniyyata aikin Hajjin shekarar 2026 da su fara shirin biyan kudaden ajiya.

Kiran ya biyo bayan taron da Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta gudanar tare da hukumomin Alhazai na jihohi, inda aka bayar da shawarar ajiyar naira miliyan 8 da rabi ga masu niyyar zuwa aikin Hajji, kafin a sanar da hakikanin kudin aikin Hajjin shekarar 2026.

A cikin wata sanarwa, mai magana da yawun hukumar, Yunusa Mohammed Abdullahi, ya shawarci wadanda ba su da fasfo da su gaggauta zuwa Hukumar Shige da Fice ta Kasa domin yin nasu, yana mai cewa shi ne ake amfani da shi wajen hada takardun tafiya.

Najeriya ta sake samun kujeru 95,000 daga Masarautar Saudiyya domin aikin Hajjin 2026, ana kuma sa ran  jihar Kaduna za ta sake samun yawan kujerun da aka saba bata.

Yunusa Mohammed ya kuma bayyana cewa hukumar za ta sanar da maniyyata lokacin da za a fara yin rajista a Jihar Kaduna.

 

Safiyah Abdulkadir 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Yadda matasa ke bayar da gudunmawa ga ci-gaban al’umma
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
  • Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna
  • Hukumar Alhazai ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Maniyyatan Aikin Hajjin 2026 Su Fara Biyan Kudaden Ajiya
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
  • Gwamna Bago Ya Kaddamar da Katafaren Kamfanin sarrafa Man Kade A Afirka.
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
  • Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata
  • Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Katin Duba Sakamakon Jarabawa Kyauta Ga Ɗalibai