Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa ya tunasar da karamar hukumar Roni game da bukatar gina wani rukuni mai dauke da ajujuwa guda biyu ga makarantun ‘ya’yan Fulani makiyaya domin inganta rayuwar su.

Shugaban kwamatin, Alhaji Aminu Zakari, ya yi wannan kiran a karshen ziyarar kwanaki biyu da kwamatin ya yi a karamar hukumar Roni.

Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa a majalisar dokokin jihar Jigawa, ya ce tanadin gina ajujuwan ga makarantun ‘ya’yan Fulani makiyaya na kunshe cikin kasafin kudin kananan hukumomi.

Ya kuma bayyana gamsuwa da bin kyakkyawan tsarin sadarwa tsakanin bangaren zartaswa da na kamsiloli ta yadda bangaren kamsiloli ya nemi bayani kan jerin ayyukan raya kasa da karamar hukumar ta ke yi a rubuce, bangaren zartaswa kuma ya mayar da jawabi a rubuce.

 

Da ya ke mika rahoton Karamin kwamatin da aka dorawa nauyin duba ayyukan raya kasa da karamar hukumar Roni ta gudanar daga watan Oktobar 2024 kawo yanzu, wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari ya duba aikin kwaskwarima ga shaguna guda shida da karamar Roni ta ci gado a garin Kazaure.

Kazalika, Alhaji Usman Tura Wanda ke tare da Wakilin mazabar Kiyawa Alhaji Yahaya Muhammad Andaza ya kuma duba aikin gyaran karamin asibiti da kuma ginin bandaki a garin Tuntube da aikin ginin filin wasannin gargajiya da runfunan kasuwa guda biyu da kasuwar shanu a yankin Daneji na garin Sankau da shataletale a Rani Kan Hawa.

Ya yabawa shugaban karamar hukumar Roni bisa kokarinsa na biyan diyyar filin da aka gina asibitin Tuntube, wadda aka yi jinkirin biya fiye da shekaru 15, da ma kokarinsa na karbo gonakin da ‘yan karamar hukumar Makoda ta jihar Kano su ka ci iyakar karamar hukumar Roni.

Da yake mayar da jawabi, shugaban karamar hukumar Roni Dakta Abba Ya’u ya ce zai shirya taro domin ganawa da manyan ma’aikata da nufin tattaunawa Kan matakan da su ka dace a bi wajen aiwatar da shawarwari da gyare gyaren da kwamatin ya bayar domin cigaban karamar hukumar.

Sauran ‘yan kwamatin sun hada da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama da na Kiyawa da na Buji da na Kanya, sai kuma Oditoci biyu da mataimakin sakataren kwamatin Sadiq Muhammad.

 

Usman Mohammed Zaria

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar Roni a karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Mai shekara 70 ya kashe ƙanwarsa kan gadon gona a Jigawa

Wani mummunan lamari na kisan gilla ya afku a ƙauyen Galadanchi da ke Ƙaramar hukumar Dutse a Jihar Jigawa.

Rundunar ’yan sandan jihar ta kama wani tsoho mai shekara 70 bisa zargin kashe ƙanwarsa saboda rikici kan filin gado.

Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu An gano wasu bama-bamai 56 da ISWAP suka binne a Borno

Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar y’an sandan jihar, SP Lawan Adam Shi’isu ya fitar ya ce tsohon mai suna Adamu Yakubu – ɗan asalin ƙauyen Galadanchi ne wanda ya samu saɓani da ƙanwarsa mai suna Hannatu Hashimu, mai shekara 45, kan rabon gadon wata gona da suka gada.

Bayanan binciken farko da ’yan sanda suka fitar, ya nuna cewa wanda ake zargin ya jefi ƙanwar tasa da sanda ne a lokacin da suka yi zazzafar gardama a tsakaninsu kan rabon gadon.

Rikicin dai ya fara ne kamar da rashin jituwar musayar kalamai, amma ya rikiɗe zuwa tashin hankali.

Inda tsohon da ake zargin ya kai wa ƙanwar tasa duka da sanda, wanda ya yi sanadin mutuwar Hannatu Hashimu. Kamar yadda bayanan ’yan sanda ya  nuna.

”Marigayiyar ta fita daga gidan a fusace, ta koma gidan aurenta, da zuwanta kuma ta faɗi ta suma, nan take aka garzaya da ita asibiti inda likitocin Babban Asibitin Dutse suka tabbatar da mutuwarta”, cewar ’yan sandan.

Rundunar ’yan sandan sun kama tsohon da ake zargin, inda yanzu haka suke gudanar da bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatan MDD Masu Kula Da Ayyukan Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Su Fice daga Kasar
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
  • Mai shekara 70 ya kashe ƙanwarsa kan gadon gona a Jigawa
  • Abba ya naɗa Ahmed Musa a matsayin Babban Manajan Kano Pillars
  • NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku
  • Majalisar Jigawa Ta Isa Roni A Ci Gaba Da Rangadin Kananan Hukumomi
  • Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA
  • Tsohon golan Super Eagles, Peter Rufai ya mutu
  • ’Yan Majalisar Wakilai bakwai na Akwa Ibom sun koma APC