Majalisar Jihar Jigawa Ta Bukaci Karamar Hukumar Roni Ta Samar Da Karin Ajujuwa Ga Fulani Makiyaya
Published: 6th, July 2025 GMT
Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa ya tunasar da karamar hukumar Roni game da bukatar gina wani rukuni mai dauke da ajujuwa guda biyu ga makarantun ‘ya’yan Fulani makiyaya domin inganta rayuwar su.
Shugaban kwamatin, Alhaji Aminu Zakari, ya yi wannan kiran a karshen ziyarar kwanaki biyu da kwamatin ya yi a karamar hukumar Roni.
Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa a majalisar dokokin jihar Jigawa, ya ce tanadin gina ajujuwan ga makarantun ‘ya’yan Fulani makiyaya na kunshe cikin kasafin kudin kananan hukumomi.
Ya kuma bayyana gamsuwa da bin kyakkyawan tsarin sadarwa tsakanin bangaren zartaswa da na kamsiloli ta yadda bangaren kamsiloli ya nemi bayani kan jerin ayyukan raya kasa da karamar hukumar ta ke yi a rubuce, bangaren zartaswa kuma ya mayar da jawabi a rubuce.
Da ya ke mika rahoton Karamin kwamatin da aka dorawa nauyin duba ayyukan raya kasa da karamar hukumar Roni ta gudanar daga watan Oktobar 2024 kawo yanzu, wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari ya duba aikin kwaskwarima ga shaguna guda shida da karamar Roni ta ci gado a garin Kazaure.
Kazalika, Alhaji Usman Tura Wanda ke tare da Wakilin mazabar Kiyawa Alhaji Yahaya Muhammad Andaza ya kuma duba aikin gyaran karamin asibiti da kuma ginin bandaki a garin Tuntube da aikin ginin filin wasannin gargajiya da runfunan kasuwa guda biyu da kasuwar shanu a yankin Daneji na garin Sankau da shataletale a Rani Kan Hawa.
Ya yabawa shugaban karamar hukumar Roni bisa kokarinsa na biyan diyyar filin da aka gina asibitin Tuntube, wadda aka yi jinkirin biya fiye da shekaru 15, da ma kokarinsa na karbo gonakin da ‘yan karamar hukumar Makoda ta jihar Kano su ka ci iyakar karamar hukumar Roni.
Da yake mayar da jawabi, shugaban karamar hukumar Roni Dakta Abba Ya’u ya ce zai shirya taro domin ganawa da manyan ma’aikata da nufin tattaunawa Kan matakan da su ka dace a bi wajen aiwatar da shawarwari da gyare gyaren da kwamatin ya bayar domin cigaban karamar hukumar.
Sauran ‘yan kwamatin sun hada da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama da na Kiyawa da na Buji da na Kanya, sai kuma Oditoci biyu da mataimakin sakataren kwamatin Sadiq Muhammad.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar Roni a karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
’Yan bindiga sun sace Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Honarabul Samaila Bagudu, a garinsu da ke Ƙaramar Hukumar Bagudu.
Rahotanni sun bayyana cewa ’yan bindigar sun mamaye garin Bagudu ne da yammacin ranar Juma’a tare da yin harbe-harbe don tsorata al’umma.
Maharan sun yi awon gaba da ɗan majalisar ne a kan hanyarsa ta dawowa daga masallaci bayan ya an idar da sallah masallaci a garin na Bagudu.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya ce an sanar da hukumomin tsaro, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da kuɓutar da Mataimakin Shugaban Majalisar.