Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
Published: 5th, July 2025 GMT
Kungiyar Falasdinawa ta Jihadul Islami a Gaza, ta bada sanarwan halaka ko jikatar sojojin yahudawan Sahyoniyya 40 a gaza a wani tarko mai sarkakiyan da suka dana masu.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Saraya Qudus” reshen soje na kungiyar Jihadul Islamim yana fadar haka a jiya Jumma’a.
Daya daga cikin kwamnadojin dakarun ya bayyana cewa da farko halakar yahudawan ta faru ne a garin Gaza a kuma unguwar shuja’iyya. Inda da farko suka halaka sojojin yahudawa kimani 10 a cikin wani ginin da suka shiga cikinsa tare da amfani da makamai mai linzami, sannan a wani gidan
Sannan waso sojojin kimani 20 sun halaka ko sun ji rauni a lokacin dakarun suka yi am,fani da makamin TBG wanda yake watsa isakar gas da ruwa da kuma gari a inda ya fashe don kona jikin wadanda ya fashe a cikinsu.
Na uku kuma sun tana nakiyoyi masu karfi kan tankar yaki dauke da akalla sojojin yahudawa 6 suka kone .
Labarin ya kara da cewa sojojin makiya a irin wannan halin sun kasa daukar wani mataki in banda gudu daga wurin. Daga karshe ba abinda zaka gani sai gawakin sojoji a waste a yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace dabbobi a Katsina
’Yan bindiga sun kashe mutum ɗaya tare da sace dabbobi da dama a wasu ƙauyuka da ke Ƙaramar Hukumar Kankia a Jihar Katsina.
Lamarin ya faru ne a daren ranar Litinin, inda aka kashe wani mazaunin ƙauyen Kwadawa da ke yankin Gachi, yayin da wani kuma ya jikkata.
Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincikeShaidu sun ce kimanin ’yan bindiga 100 ne suka kai harin, inda suka kuma mamaye ƙauyen Bogga; ƙauyen Fulani da ke kan hanyar Kankia zuwa Ingawa.
Sakamakon haka, mazauna ƙauyukan Bogga, Taiba Badole, Arahiya Kwandawa, Rumawa, Gangara da Rugar Bindo duk da ke yankunan Gachi da Fakuwa/Kafindangi, sun tsere daga gidajensu saboda tsoron hare-hare.
Wasu mazauna yankin sun bayyana cewa ’yan bindigar sun koma Kankia bayan da aka samu yarjejeniyar zaman lafiya a wasu ƙananan hukumomi maƙwabta, lamarin da ya sa suka faɗaɗa hare-harensu zuwa yankunan Charanchi da Kusada.
Wani mazaunin yankin mai suna Haladu Badole ya ce: “Kwana uku da suka gabata mun fara lura da motsin wasu mutane da ba mu saba gani ba, sannan a daren jiya suka kai hari suka kwashe dabbobinmu.”
Mutanen yankin sun roƙi hukumomi da su tura jami’an tsaro domin kare rayukansu da dukiyoyinsu.
Yankin gabashin Kankia, ya kasance cikin zaman lafiya, sai dai kwanan nan an fara samun hare-hare a yankunan Rimaye, Magam, Sukuntuni, Gyaza da Kunduru.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Sadik Aliyu, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Amma ya ce rundunar ta fara bincike kuma tana ƙoƙarin samar da zaman lafiya a yankin.