Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
Published: 5th, July 2025 GMT
Kungiyar Falasdinawa ta Jihadul Islami a Gaza, ta bada sanarwan halaka ko jikatar sojojin yahudawan Sahyoniyya 40 a gaza a wani tarko mai sarkakiyan da suka dana masu.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Saraya Qudus” reshen soje na kungiyar Jihadul Islamim yana fadar haka a jiya Jumma’a.
Daya daga cikin kwamnadojin dakarun ya bayyana cewa da farko halakar yahudawan ta faru ne a garin Gaza a kuma unguwar shuja’iyya. Inda da farko suka halaka sojojin yahudawa kimani 10 a cikin wani ginin da suka shiga cikinsa tare da amfani da makamai mai linzami, sannan a wani gidan
Sannan waso sojojin kimani 20 sun halaka ko sun ji rauni a lokacin dakarun suka yi am,fani da makamin TBG wanda yake watsa isakar gas da ruwa da kuma gari a inda ya fashe don kona jikin wadanda ya fashe a cikinsu.
Na uku kuma sun tana nakiyoyi masu karfi kan tankar yaki dauke da akalla sojojin yahudawa 6 suka kone .
Labarin ya kara da cewa sojojin makiya a irin wannan halin sun kasa daukar wani mataki in banda gudu daga wurin. Daga karshe ba abinda zaka gani sai gawakin sojoji a waste a yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ayatullahi Khatami Ya Ce Hukuncin Da Ya Cancanci Trump Da Netanyahu Shi Ne Kisa Saboda Zubar Da Jinin Bil’Adama
Limamin da ya jagoranci sallar Juma’a a birnin Tehra mya bayyana cewa: Hukuncin shari’a da ya hau kan Trumpm da Netanyahu shi ne kisa
Limamin da ya jagoranci sallar juma’a a birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran a yau ya bayyana cewa: Amurka da karen da suka horar sun yi barazana ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma wannan wauta ce. Hakika dokar Musulunci ta Trump da Netanyahu ita ce mutuwa. Sun kashe mutane fiye da 55,000 a Gaza. Su suka kai Qasim Sulaimani da yin shahada da sauran abokansa. Su ne masu aiwatar da kisan kai da ayyukan fasadi a duniya. Sun yi wa Jagoran juyin juya halin Musulunci da al’ummar Iran barazana. Abin farin cikin shi ne, dukkanin hukumomin addini na birnin Qum da Najaf sun tashi tsaye tare da yin Allah wadai da wannan gurbatacciyar tunani. Sannan a baya-bayan nan Ayatullah Nasir Makarem Shirazi da Ayatullahi Nuri sun yi tofin Allah tsine kan wannan barazana da bayyana hakan a matsayin shelanta yaki.
Hujjatul-Islam Ahmad Khatami a cikin hudubar sallar juma’ar a birnin Tehran, yayin da yake ishara da harin da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta kai harin wuce gona da iri kan kasar Iran ya ce: martani da dakarun Iran suka mayar kan gwamnatin yahudawan sahayoniyya abu ne da ke gwada karfinsu na mayar da martini kan dukj wani mai girman kai da dagawa.
AYatullahi Hatami ya kara da cewa: Son kasa da kare Musulunci so ne ga Allah. Kuma kishin kasa wani bangare ne na Imani, don haka ya karfafa al’umma kan Shirin kare kasarsu da kimar daular Musulunci daga duk wani dan mamaya mai kiyayyaya da kyawawan dabi’un addini.