Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba
Published: 5th, July 2025 GMT
Wasu ƙungiyoyin mata a ƙauyukan Bendeghe-Ekiem da Abiya da ke Ƙaramar Hukumar Etung, a Jihar Kuros Riba, sun yi barazanar gudanar da zanga-zangar tsirara idan gwamnati ba ta janye ƙudirin sayar da gonakin koko ba.
Matan sun ce wannan shawara da gwamnati ta ɗauka ba su aminta da ita ba, domin gonakin koko su ne tushen rayuwarsu, wanda da su suke cin abinci, suke biya wa ’ya’yansu kuɗin makaranta.
Aminiya ta samu rahoton cewa gwamnati na shirin sayar da hannun jarinta a wasu manyan gonakin koko da ke wannan yanki, wanda hakan ya fusata matan da sauran al’ummar ƙauyukan da abin ya shafa.
Majiyarmu ta ce, “Idan gwamnati ta sayar da hannun jarinta, to tamkar hana mu cin moriyar aikin gonarmu ne. Wannan mataki ya saɓa wa yarjejeniyar da aka taɓa yi a baya.”
A ƙarshen mako, wasu daga cikin matan sun gudanar da zanga-zanga r lumana don nuna rashin amincewarsu da wannan ƙudiri.
Sai dai duk da ƙoƙarin sasanci daga Ma’aikatar Ayyukan Gona ta jihar, matan sun bai wa gwamnati wa’adin mako biyu ta janye shirin, ko kuma su fito su yi zanga-zangar tsirara.
Shugabannin ƙungiyoyin matan; Ntunkai Mary Obi da Cif Helen Ogar, sun roƙi Kwamishinan Ayyukan Gona, Johnson Ebokpo, da ya kai wa gwamnan kokensu, domin a samu mafita kan lamarin.
“Mun bai wa gwamnati mako biyu ta janye wannan ƙudiri ko kuma a zauna da shugabanninmu domin a cimma matsaya.”
Baya ga matan, wasu shugabannin matasa da dattawan yankin irin su Kwamared Tandu Kingsley da Mista Etta Atu-Ojua, sun goya matan baya.
Sun ce: “Idan gwamnati ta sayar da gonakin, matasa ba za su ƙara samun abin yi ba, kuma hakan zai jefa wasu cikin ayyukan daba da sata.”
Sun buƙaci gwamnatin ta sake nazari da idon basira, domin kada al’umma su shiga cikin ƙalubalen rayuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barazana
এছাড়াও পড়ুন:
Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
Idan ka duba tarihin duniya gabadaya da tarihin annabawa, tarihi ne na wayewar duniya tun daga Annabi Nuhu (S.A.) har zuwa Manzon Allah (S.A.W.) kamar duniya tana ‘yar makaranta ce ta fara da Nazare, ta zo Firamare zuwa Sakandire har zuwa Jami’a, sannan aka yaye ta, yanzu da zuwan Manzon Allah an yaye duniya, yanzu duniya ba ta bukatar sai an aiko annabi, ba ta bukata sai an aiko ma’aiki, a’a wanna abu da Manzon Allah ya zo da shi za mu iya kafa dalili da shi mu shirya kanmu ba sai da annabi ba.
Wannan abu da Manzon Allah ya zo da shi yanzu ya kafa dalili da shi, da shi muka karantar da kanmu ba sai da Annabi ba, wannan abu da ya zo da shi za mu iya aiki da shi mu zauna lafiya, mu haramta abin da Allah Ya haramta. Yanzu kamar an yaye mu ne daga Jami’a tun daga jami’a tun daga zamanin Annabi Nuhu (A.S.) har ya zuwa Annabi Muhammadu (S.A.W.). idan ka faro duniya daga farkon ma’aika, duniya ta faro ne daga sanin wuta wato yadda za a yi amfani da wuta. Dan adam na farko ya ji tsoron wuta wasu sun tafi a kan cewa farkon abin da Dan Adam ya fara bautawa shine wuta, wanda ita ta fara ba shi tsoro ba wai ya iya kunnawa ba amma ya ga daki ya kama da wuta, dubi irin zamanin nan duk da motocin kashe gobara haka daji zai kama da wuta ta gagare su balle ka koma zamani da shekara miliyan kaza wanda dan Adam bai ma santa ba sai dai ya ga daki ya kama da wuta (wata ay ana cewa) “Allahn da ya sa muku wuta a ciki koren ganye ko koriyar bishiya”, malamai na cewa bishiya mai yado wanda ake kunna wuta, toh wannan abu ne ya sa idan wuta ta kama aka kasa shawo kanta sai mutane su tsorata su ce wai meye wannan, meye ya kunna wannan wutar? Suka ga to lallai wannan duniyar da suke ciki akwai wani abu a boye, gwara su bauta wa abin nan na boye fa, don ya kiyaye su daga wanna wutar har suka fara bauta mata da yanka dabbbobi don ta kiyaye su, gaba daya dai har ta soma gasa wasu abubuwa na dabbobi, idan wutar ta mutu suka zo wurin su ji kamshin ya bambanta, idan sun sa a baki su ji dadinsu ya banbanta. Toh tana daya daga cikin abin da ta koya wa dan Adam wayewa.
Da dan Adam ya waye, wuta tana daya daga cikin abin da ya wayar da dan Adam kuma idan ka lura yau wuta ita ke biye da mu duk wasu kere-kere za ka ga daga wuta ne, abin da muke tsoro kuma shi ne babban abin amfani, toh a haka dai dan Adam har ya iya kera wutar da kansa. Kamar yadda Allah ya fada mana cikin ‘ya’yan Adam da daya ya kashe daya ya rasa yadda zai yi, a haka ne har dan Adam ya san yadda zai binne dan’uwansa har zuwa zamanin Annabi Idirisu sama ta soma magana da kasa, Allah ya soma aiko ma dan Adam da mala’ika, su ne wadannan mutane da muke cewa ko akwai su a duniyar wata ko mutanen sama, Turawa duk sun rubuta wannan abu, sun zana wannan abu sai ga shi irin wannan jirage ne wanda ake cewa na duniyar sama, daya daga ciki Annabi Sha’ayahu yake cewa ga wani abu ya sauko kasa mai kara iri kaza.
Tun daga zamanin Annabi Idris mala’iku ne suka kawo sako suke yin magana da mutanen kasa, su ake cewa tatsuniyoyi na duk al’umma, tatsuniya ne a wajenmu amma su gaske ne a wajensu, su ce mutane sun sauko musu daga sama, har aka zo zamanin Annabi Nuhu ya tabbatar, da ya zo ya fada wa mutane suka ce ba su yarda ba, ba mu ji wannan wajen iyayenmu ba, haka aka ci gaba har zuwa zamanin Annabi Hudu dan Adam ya fara hore dabbobi, dabbar da dan Adam ya fara horewa shi ne kare, kuma ya hore dabbobin da zai ci, zai iya gane wannan dabbar ba zai ci ba wannan zai ci, wannan zai iya zama da ita lafiya, wannan ba zai iya zama da ita ba, daga nan dan Adam ya fara gini, ya dan kwakule kasa ya yi kogo ya shiga.
Har ya zuwa Annabi Salihu, har dan Adam ya fara fahimtar wannan kwayar da take fitowa a kasa, wannan zan iya ci in rayu, wannan kwayar kuma ba a cin ta, har ya soma tunanin toh wannan kwayar ya zan ajiye ta zuwa nan gaba in sake shuka ta, haka dan Adam har ya soma yin noma a aikace don ya rayu. Allah ya gaya mana wannan yana daga cikin ayoyin Allah (kamar yadda ya zo a aya) “arziki yana daga cikin kasa da abin da kasa take tsirarwa da abin da hannunka yake aikatawa” kamar sana’a ko noma ko nema. Toh ka ga a nan babu zancen ka ce ba za ka yi nema ba, duk abin da kake nema idan ka juya kasa za ka same shi, duka kasar da ta rike noma da sana’a za ku ga sun fi arziki, Allah ga shi ya gaya mana idan kafiri ya fi ka arziki sai dai ka nema a wajensa, don haka mu dogara da Allah shi ke azurtawa, ga ka’idoji nan ya fada mana, nema, kiwo abubuwa duk gabaki daya.
Za mu ci gaba a mako mai zuwa in sha Allahu.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA