Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba
Published: 5th, July 2025 GMT
Wasu ƙungiyoyin mata a ƙauyukan Bendeghe-Ekiem da Abiya da ke Ƙaramar Hukumar Etung, a Jihar Kuros Riba, sun yi barazanar gudanar da zanga-zangar tsirara idan gwamnati ba ta janye ƙudirin sayar da gonakin koko ba.
Matan sun ce wannan shawara da gwamnati ta ɗauka ba su aminta da ita ba, domin gonakin koko su ne tushen rayuwarsu, wanda da su suke cin abinci, suke biya wa ’ya’yansu kuɗin makaranta.
Aminiya ta samu rahoton cewa gwamnati na shirin sayar da hannun jarinta a wasu manyan gonakin koko da ke wannan yanki, wanda hakan ya fusata matan da sauran al’ummar ƙauyukan da abin ya shafa.
Majiyarmu ta ce, “Idan gwamnati ta sayar da hannun jarinta, to tamkar hana mu cin moriyar aikin gonarmu ne. Wannan mataki ya saɓa wa yarjejeniyar da aka taɓa yi a baya.”
A ƙarshen mako, wasu daga cikin matan sun gudanar da zanga-zanga r lumana don nuna rashin amincewarsu da wannan ƙudiri.
Sai dai duk da ƙoƙarin sasanci daga Ma’aikatar Ayyukan Gona ta jihar, matan sun bai wa gwamnati wa’adin mako biyu ta janye shirin, ko kuma su fito su yi zanga-zangar tsirara.
Shugabannin ƙungiyoyin matan; Ntunkai Mary Obi da Cif Helen Ogar, sun roƙi Kwamishinan Ayyukan Gona, Johnson Ebokpo, da ya kai wa gwamnan kokensu, domin a samu mafita kan lamarin.
“Mun bai wa gwamnati mako biyu ta janye wannan ƙudiri ko kuma a zauna da shugabanninmu domin a cimma matsaya.”
Baya ga matan, wasu shugabannin matasa da dattawan yankin irin su Kwamared Tandu Kingsley da Mista Etta Atu-Ojua, sun goya matan baya.
Sun ce: “Idan gwamnati ta sayar da gonakin, matasa ba za su ƙara samun abin yi ba, kuma hakan zai jefa wasu cikin ayyukan daba da sata.”
Sun buƙaci gwamnatin ta sake nazari da idon basira, domin kada al’umma su shiga cikin ƙalubalen rayuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barazana
এছাড়াও পড়ুন:
An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
Ƙungiyar Malaman Makarantu ta Najeriya (NUT) reshen Jihar Gombe, ta ziyarci shugaban ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomi na jihar, Barista Sani Ahmad Haruna, a ofishinsa da ke Gombe.
Shugaban ƙungiyar, wanda shi ne shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, ya bayyana cewa gwamnati da shugabannin ƙananan hukumomi za su ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen inganta walwalar malamai.
Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyiYa ce: “Ba za mu taɓa barin malamai su shiga cikin matsanancin hali ba. Za mu duba matsalolinsu domin tabbatar da walwalarsu da ci gaban ilimi a jihar.”
Sani, ya kuma yaba da yadda NUT ke tattaunawa cikin lumana da kawo shawarwari maimakon ɗaukar matakan da za su iya kawo tsaiko ga harkar ilimi.
A nasa jawabin, shugaban NUT na jihar ya ce sun kai ziyarar ne domin tattauna matsalolin da malamai ke fuskanta, musamman na makarantun firamare da ƙananun sakandare da ke ƙarƙashin kulawar ƙananan hukumomi.
Ya ƙara da cewa manufar NUT ita ce samar da fahimtar juna da haɗin kai tsakaninsu da shugabannin ƙananan hukumomi domin gano hanyoyin magance matsaloli cikin lumana.