Aminiya:
2025-07-31@12:23:04 GMT

Tsohuwar ɗaliba ta kai ƙarar makarantar da ta kammala

Published: 17th, March 2025 GMT

Wata matashiya mai suna Aleysha Ortiz ’yar shekara 19 da ke Jihar Connecticut a Amurka ta dauki matakin shari’a a kan tsohuwar makarantar sakandaren gwamnatin da ta yi saboda gazawarta ta hanyar ba ta damar kammala karatu “da sakamako mai daraja” duk da ta kasance maras ƙoƙari.

A watan Yunin shekarar bara ce, Aleysha Ortiz ta kammala karatu a Makarantar Hartford Public High School da ke Hartford, a Jihar Connecticut, inda aka karama ta, har ma ta samu gurbin karatu a kwaleji, amma yanzu ta kai karar tsohuwar makarantarta saboda sakacinta.

Gidauniyar Dangote ta ƙaddamar da rabon abincin N16bn ga talakawan Nijeriya EFCC ta kama Murja Kunya kan wulaƙanta takardun Naira

Matashiyar mai shekara 19 tana zargin makarantar da ta kammala da yin watsi da karatunta, tana mai cewa da ƙyar za ta iya riƙe fensir a hannunta kuma ƙoƙarin karatunta ya yi kama da na dalibi ɗan aji daya.

An haife ta a garin Puerto Rico, Aleysha tana fama da matsalolin koyo tun tana karama, kuma dabi’arta ta ci gaba bayan ta yi ƙaura zuwa Amurka tana ’yar shekara 5.

Ta yi iƙirarin cewa, makarantarta da kuma malaminta na musamman da aka ba ta ba su da wani amfani har sai wata guda kafin ta kammala karatunta a zango na ƙarshe lokacin da suka gudanar da ƙarin gwajin da take nema kuma suka gane cewa ba ta da ƙoƙari.

Jami’an hukumar makarantar sun shaida wa matashiyar cewa, za ta iya jinkirta karɓar takardar shaidar kammala karatunta na difiloma don sauya su da wasu ayyuka. Amma ta ƙi amincewa.

Ortiz ta bayyana wa CNN cewa, “Na yanke shawarar shigar da ƙara, yanzu lokacina ne,” inda ta ƙara da cewa, kammala karatunta da karramawa daga makarantar sakandare Hartford Public High School, wanda yawanci yana nufin ɗalibi ya nuna ƙwarewa a fannin ilimi.

Amma ta yaya Aleysha Ortiz za ta kammala karatun sakandare tare da karramawa yayin da ba ta iya karatu da rubutu ba? Ta yaya aka karɓe ta zuwa Jami’ar Connecticut?

Ta yi iƙirarin cewa, manhajojin zamani suna matuƙar taimakawa. Tana amfani da manhajojin wayar hannu don fassara rubutu zuwa murya da murya zuwa rubutu, har ma ta yi amfani da su wajen aikace-aikacen kwalejin da rubuce-rubucen da ake bukata. Kasancewarta ɗalibai kwalejin ya saka ta cikin yanayi na daban-daban.

Aleysha ta yarda cewa, inda ta daina zuwa ajin karatu a farkon Fabrairu. Ta so ta ɗauki lokaci don kula da lafiyar ƙwaƙwalwarta, amma tana fatan komawa azuzuwa nan ba da jimawa ba.

Aleysha ta ce, ta kai ƙarar tsohuwar makarantarta ce saboda tana son a tuhumi shugabanninta kan abin da ta fuskanta.

Ta yi ikirarin cewa, “ba su san abin da suke yi ba kuma ba su damu ba,” kuma tana fatan cewa, fafutukar da take yi a shari’ar zai hana wasu matasa rashin samun cikakken ilimi.

“Ni mutum ce mai matukar sha’awar karatu kuma ina son koyo,” in ji Ortiz.

“Mutane sun yi amfani da wannan damar don koyo, kuma yanzu ina kwaleji kuma ina so in yi amfani da wannan.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaliba Makaranta kammala karatu

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta ba da shawarar a soke ko kara inganta aikin titin gina hanya mai tsawon kilomita biyar a karamar hukumar Gabasawa.

Wannan mataki ya biyo bayan karɓar rahoton da Kwamitin  Majalisar kan Harkokin Jinƙai da Rage Talauci ya gabatar dangane da ambaliyar da ta afku a Zakirai, cikin karamar hukumar ta Gabasawa.

Da yake gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin, Alhaji Sule Lawan Shuwaki, ya bayyana wasu muhimman shawarwari da suka hada da: Umurtar kamfanin da ke aikin gina hanyar da ya faɗaɗa magudanar ruwa a yankin da abin ya shafa da kuma gaggauta kai agajin gaggawa ga waɗanda ambaliyar ta shafa.

Sauran shawarwarin sun haɗa da tura tawagar ƙwararru daga ma’aikatun ayyuka da muhalli na jihar don gudanar da bincike da bayar da shawarwarin fasaha.

Bayan nazari da tattaunawa mai zurfi, majalisar ta amince da rahoton baki ɗaya tare da kiran gwamnatin jihar da ta gaggauta ɗaukar mataki domin rage tasirin ambaliya a Zakirai.

A wani sabon lamari kuma, majalisar ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta gaggauta sake gina hanyar da ke haɗa Kwanar ‘Yan Mota zuwa Kwanar Bakin Zuwo zuwa Jakara, zuwa Kwanar Gabari a cikin karamar hukumar birnin Kano.

Wanda ya gabatar da kudirin, Honarabul Aliyu Yusuf Daneji, mai wakiltar mazabar Kano Municipal, ya jaddada cewa hanyar, musamman a kusa da kasuwar Kurmi, tana cikin matsanancin hali wanda ke kawo cikas ga zirga-zirga da kuma lalata harkokin kasuwanci.

Haka kuma, Alhaji Abdullahi Yahaya, mai wakiltar mazabar Gezawa, ya gabatar da kudiri na buƙatar gina titin kwalta daga Jogana zuwa Matallawa, Yamadi Charo da Daraudau.

Ya ce hanyar ba ta dadin bi a lokacin damina, inda al’ummar yankin ke ɗaukar matakin kansu ta hanyar cike ramuka da yashi da itace.

Kudirin ya samu goyon bayan Jagoran Masu Rinji a Majalisar, Alhaji Zakariyya Abdullahi Nuhu, tare da cikakken goyon bayan ‘yan majalisar baki ɗaya.

Sauran kudirori da aka amince da su a zaman sun haɗa da: Gina titi daga Dalawada zuwa Gazobi a karamar hukumar Tudun Wada da kuma sake gina hanyar Fanisau a Ungogo.

 

Daga Khadijah Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa