Aminiya:
2025-11-02@06:07:15 GMT

Tsohuwar ɗaliba ta kai ƙarar makarantar da ta kammala

Published: 17th, March 2025 GMT

Wata matashiya mai suna Aleysha Ortiz ’yar shekara 19 da ke Jihar Connecticut a Amurka ta dauki matakin shari’a a kan tsohuwar makarantar sakandaren gwamnatin da ta yi saboda gazawarta ta hanyar ba ta damar kammala karatu “da sakamako mai daraja” duk da ta kasance maras ƙoƙari.

A watan Yunin shekarar bara ce, Aleysha Ortiz ta kammala karatu a Makarantar Hartford Public High School da ke Hartford, a Jihar Connecticut, inda aka karama ta, har ma ta samu gurbin karatu a kwaleji, amma yanzu ta kai karar tsohuwar makarantarta saboda sakacinta.

Gidauniyar Dangote ta ƙaddamar da rabon abincin N16bn ga talakawan Nijeriya EFCC ta kama Murja Kunya kan wulaƙanta takardun Naira

Matashiyar mai shekara 19 tana zargin makarantar da ta kammala da yin watsi da karatunta, tana mai cewa da ƙyar za ta iya riƙe fensir a hannunta kuma ƙoƙarin karatunta ya yi kama da na dalibi ɗan aji daya.

An haife ta a garin Puerto Rico, Aleysha tana fama da matsalolin koyo tun tana karama, kuma dabi’arta ta ci gaba bayan ta yi ƙaura zuwa Amurka tana ’yar shekara 5.

Ta yi iƙirarin cewa, makarantarta da kuma malaminta na musamman da aka ba ta ba su da wani amfani har sai wata guda kafin ta kammala karatunta a zango na ƙarshe lokacin da suka gudanar da ƙarin gwajin da take nema kuma suka gane cewa ba ta da ƙoƙari.

Jami’an hukumar makarantar sun shaida wa matashiyar cewa, za ta iya jinkirta karɓar takardar shaidar kammala karatunta na difiloma don sauya su da wasu ayyuka. Amma ta ƙi amincewa.

Ortiz ta bayyana wa CNN cewa, “Na yanke shawarar shigar da ƙara, yanzu lokacina ne,” inda ta ƙara da cewa, kammala karatunta da karramawa daga makarantar sakandare Hartford Public High School, wanda yawanci yana nufin ɗalibi ya nuna ƙwarewa a fannin ilimi.

Amma ta yaya Aleysha Ortiz za ta kammala karatun sakandare tare da karramawa yayin da ba ta iya karatu da rubutu ba? Ta yaya aka karɓe ta zuwa Jami’ar Connecticut?

Ta yi iƙirarin cewa, manhajojin zamani suna matuƙar taimakawa. Tana amfani da manhajojin wayar hannu don fassara rubutu zuwa murya da murya zuwa rubutu, har ma ta yi amfani da su wajen aikace-aikacen kwalejin da rubuce-rubucen da ake bukata. Kasancewarta ɗalibai kwalejin ya saka ta cikin yanayi na daban-daban.

Aleysha ta yarda cewa, inda ta daina zuwa ajin karatu a farkon Fabrairu. Ta so ta ɗauki lokaci don kula da lafiyar ƙwaƙwalwarta, amma tana fatan komawa azuzuwa nan ba da jimawa ba.

Aleysha ta ce, ta kai ƙarar tsohuwar makarantarta ce saboda tana son a tuhumi shugabanninta kan abin da ta fuskanta.

Ta yi ikirarin cewa, “ba su san abin da suke yi ba kuma ba su damu ba,” kuma tana fatan cewa, fafutukar da take yi a shari’ar zai hana wasu matasa rashin samun cikakken ilimi.

“Ni mutum ce mai matukar sha’awar karatu kuma ina son koyo,” in ji Ortiz.

“Mutane sun yi amfani da wannan damar don koyo, kuma yanzu ina kwaleji kuma ina so in yi amfani da wannan.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaliba Makaranta kammala karatu

এছাড়াও পড়ুন:

Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya nemi sabbin hafsoshin tsaron ƙasar su zage damtse domin magance duk wata barazanar tsaro da ake fuskanta a halin yanzu da ma wadda ka iya kunnowa nan gaba.

Shugaban ya gargadi sabbin hafsoshin tsaron cewa ’yan Nijeriya sakamako kawai suke buƙata, ba uzuri ba, saboda haka dole ne su cika aikin da aka ɗora musu.

Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026 Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket

Tinubu ya bayyana hakan ne bayan bikin ƙara wa sabbin hafsoshin tsaron da shugabannin rundunonin soji girma da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa yau Alhamis a Abuja.

A cewarsa, “Barazanar tsaro na ƙara sauyawa a kodayaushe, kuma abin da ya fi damun gwamnatinmu shi ne ɓullar sababbin ƙungiyoyin ’yan bindiga a Arewa ta Tsakiya, da Arewa maso Yamma, da wasu sassa a Kudanci.”

A ranar Laraba ce Majalisar Dattawa da ta Wakilai suka amince da naɗin Laftanar Janar Olufemi Oluyede a matsayin Babban Hafsan Tsaro; Manjo Janar Waidi Shaibu a matsayin Hafsan Sojan Ƙasa; Rear Admiral Idi Abbas Hafsan Sojan Ruwa; Air Marshall Kennedy Aneke Hafsan Sojan Sama; da Manjo Janar Emmanuel Undiendeye a matsayin Shugaban Tattara Bayanai na Soja.

“Ba zai yiwu mu ƙyale wannan sabuwar barazanar ta ci gaba ba. Dole ne mu ɗauki mataki da wuri. Mu sare kan macijin.

“’Yan Najeriya suna sa rana ganin sakamako, saboda haka babu wani uzuri da za su karɓa. Ina kuma kira da ku kasance masu dabaru da hangen nesa da kuma jarumta.

“Mu kasance mun tari hanzarin duk waɗanda ke neman tayar da zaune tsaye a ƙasarmu,” in ji Tinubu.

Yayin bikin, an ƙara wa Olufemi Oluyede muƙami zuwa Janar, Waidi Shaibu zuwa Laftanar Janar, Idi Abbas zuwa Vice Admiral, da Kevin Aneke zuwa Air Vice marshall, da kuma Emmanuel Undiendeye zuwa Laftanar Janar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri