2027: Ana raɗe-raɗin Sanata Lamiɗo zai fice daga APC zuwa ADC
Published: 6th, July 2025 GMT
Jita-jita ta fara ƙarfi cewar Sanata Ibrahim Lamiɗo da ke wakiltar Sakkwato ta Gabas a Majalisar Dattawa, na shirin ficewa jam’iyyar APC zuwa ADC.
Wannan jita-jita ta fara ƙarfi ne bayan da wasu ‘yan siyasa suka haɗu don kafa sabuwar jam’iyya mai suna ADC da nufin kayar da APC a zaɓen 2027.
Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba Kwankwaso ba zai yi mana takara a 2027 ba — NNPPA cewar wasu, Sanata Lamiɗo ba ya mu’amala da gwamnatin APC a jihar inda alaƙarsa ta fi ƙarfi da ‘yan adawa.
Wannan ne ya sa ake ganin ba zai tsaya takara a APC ba a 2027.
Wani ɗan siyasa da ya nemi a sakaya sunansa ya ce Sanata Lamiɗo ba ya ga maciji da Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko da Gwamna Ahmad Aliyu.
A cewarsa, “Sama da shekara ɗaya ba mu ga Sanata Lamiɗo a taron gwamnati ko na APC ba. Don haka ba za mu yi mamakin ficewarsa ba.”
Wani magoyin bayan APC, Kabiru Wurno, ya ce yana da tabbacin cewa Sanatan zai koma ADC.
“Lamiɗo yana son sake tsayawa takara a 2027, amma da wuya APC ta ba shi dama saboda ba ya tare da manyan jagororinta. Dole ya nemi wata hanya.”
Shu’aibu Muhammad daga Sabon Birni, ya bayyana rashin jin daɗinsa kan yiwuwar ficewar Sanatan.
“Da zai shirya da Wamakko, da za su yi ƙarfi tare. Siyasar Gabas tana buƙatar haɗin kai.”
Shi kuwa Ya’u Muhammad daga Goronyo ya ce, “Idan har Sanata Lamiɗo zai fice daga APC, muna tare da shi. Shi mutum ne da ke tallafa wa matasa da marasa galihu.”
Wani makusancin Sanatan ya ce ba zai ce uffan kan lamarin ba, zai bar Sanatan ya yi ƙarin haske.
Sai dai duk da ƙoƙarin jin ta bakin Sanata Lamiɗo haƙar Aminiya ba ta cimma ruwa ba.
Yanzu dai jama’a da dama na dakon jiran hukuncin da Sanatan zai ɗauka kafin babban taron jam’iyyar ADC da ke tafe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sakkwato Takara Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta hana yunqurin fasa wani shago da wasu vata-gari suka yi qoqarin yi a Unguwar Buba Shongo da ke cikin birnin Gombe, inda ta qwato wani babur da kayan da ake zargin an yi niyyar amfani da su wajen fasa shagon.
A cewar sanarwar da mai Magana da Yawun Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, lamarin ya faru ne da misalin qarfe 3:00 na safiyar Litinin, 1 ga Watan Yuli, 2025, lokacin da jami’an Operation Hattara ke kan sintiri a daren.
Jami’an sun hango wasu mutane da ba a san ko su wane ne ba suna qoqarin fasa wani shago mallakin wani Muhammadu Adamu Musa, mai shekara 42 da haihuwa.
Da vatagarin suka hango motar sintirin ‘yan sanda na qaratowa, sai suka tsere suka bar shagon ba tare da cimma burinsu ba.
Kayan da aka samu a wurin sun haxa da baqin babur qirar Yamaha mai lamba GME 480 VN da wani qarfe na tanqwara qoafa da takalmin roba guda xaya.
“Dukkan kayan da aka qwato suna hannun ‘yan sanda, kuma bincike yana ci gaba a kan zargin haxa baki da yunqurin aikata laifi,” in ji sanarwar.
Rundunar ta bayyana cewa wannan lamari ya qara tabbatar da cewar dokar da ta takaita zirga-zirgar babura a cikin dare a faxin jihar na nan daram, domin yawan laifukan da ake aikatawa da su a wannan lokaci na dare.
Rundunar ta kuma tabbatar wa da jama’a cewa tana ci gaba da qoqari don kamo waxanda suka gudu tare da gurfanar da su a gaban shari’a.
Haka zalika, rundunar ta buqaci jama’a da su kasance masu lura da abin da ke faruwa a muhallansu tare da ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma