Aminiya:
2025-05-23@14:19:31 GMT

El-Rufai ya nemi afuwa ko mu maka shi a kotu — Gidauniyar Ɗahiru Bauchi

Published: 17th, March 2025 GMT

Gidauniyar Sheikh Ɗahiru Bauchi ta buƙaci Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, da ya nemi afuwar ɗaliban malamin bisa abin da ta kira rashin adalci da aka musu.

Idan kuwa bai yi hakan ba kafin ƙarshen watan Ramadan, za su maka shi a kotu.

An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalma

Wannan na ƙunshe ne a wata takarda da gidauniyar ta fitar, wadda Sayyadi Aliyu Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya sanya wa hannu.

A cewar takardar, dole ne El-Rufai ya fito ya yarda da laifinsa sannan ya nemi afuwar gidauniyar, ɗalibanta da jagoranta, Sheikh Ɗahiru Bauchi.

Gidauniyar ta zargi tsohon gwamnan da bayar da umarni ga jami’an tsaro don su kai samame a makarantun tsangayar Sheikh Ɗahiru Bauchi, inda aka kama wasu ɗaliban karatun Alƙur’ani har zuwa gidansa.

Har yanzu, akwai ɗaliban da ba a san inda suke ba.

Sayyadi ya bayyana cewa an yi hakan ne da gangan domin a tozarta Sheikh Ɗahiru Bauchi da kuma hana ci gaban ilimin addini da ya ke yi.

Ya ce idan har El-Rufai bai nemi afuwa ba kafin ƙarshen Ramadan, za su kai ƙararsa ga Shugaban Ƙasa, ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam, da kotu.

Idan kuwa duka ba su yi musu adalci ba, za su mika ƙarar ga Allah ta hanyar addu’a.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gidauniya Neman Afuwa Sheikh Ɗahiru Bauchi Sheikh Ɗahiru Bauchi

এছাড়াও পড়ুন:

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

Amma kuma kariyar ciniki ba za ta taimaka ga raya sana’o’i da masana’antu a duniya ba. Idan mun lura, a cikin shekaru 10 da suka wuce, yadda kasar Amurka ta dauki matakai na kare sana’o’in samar da karafa, a maimakon ya hana raguwar guraben ayyukan samar da karafa, sai ya haifar da karuwar kudaden da sana’o’i masu alaka suka kashe. Haka al’amarin yake ma ta fannin samar da sassan na’urorin laturoni na Chips da fasahohin kirkirarriyar basira, domin rashin yin takara da hadin gwiwa da sauran kasashe ba zai haifar da da mai ido ba, illa koma baya da illoli ga sana’o’i masu alaka.

A bangaren kasar Sin kuma, yadda kasar Amurka ke yi mata kafar ungulu don dakile ci gabanta, ya sa wa kamfanonin kasar kaimin gaggauta kirkire-kirkire, don neman tsayawa da kafafuwansu a fannin kimiyya. Idan ba mu manta ba, a farkon bana, kamfanin DeepSeek mai nazarin fasahar kirkirarriyar basira na kasar Sin ya fitar da tsarin R1 da ingancin aikinsa ya kai matsayin na sauran tsarukan AI masu matsayin koli na duniya. Har ma jaridar Financial Times ta kasar Burtaniya ta yi sharhin cewa, babban kuskure ne ga Amurka yadda take neman dakile ci gaban kasar Sin. Abubuwan da suka wakana a tarihi sun shaida mana cewa, ci gaban fasahohi su kan samu ne daga rikici da takara da juna, a maimakon zaman walwala. Ita kuma tsohuwar mukaddashiyar mai mataimaka wa sakataren harkokin wajen kasar Amurka, Susan Thornton, ta yi nuni da cewa, matakan kayyadewa da Amurka ta dauka, a hakika sun yi matukar samar da kuzari ga kasar Sin ta fannin kirkire-kirkire, inda Deepseek ya shaida hakan. Ta ce, “ba zai yiwu Amurka ita kadai ta mallaki fasahar kirkirarriyar basira ba, kamata ya yi gwamnatin Amurka ta yi watsi da kariyar ciniki da ma kiyayya da take wa kasar Sin, kuma ta yi hadin gwiwa da kasar, don samar da alfanu ga dukkanin bil-Adama bisa fasahar kirkirarriyar basira.”

Ma iya cewa, Madam Susan Thornton mai idon basira ce game da bunkasar sana’o’i masu alaka da fasahar kirkirarriyar basira. Lallai kawo tarnaki ga wasu ba ya kara wa mai yin hakan sauri da kuzarin tafiya. Matakan da kasar Amurka ke dauka na neman dakile ci gaban kasar Sin, ba zai haifar da kome ba, illa su sa kasar ta Sin ta kara karfinta da gaggauta ci gabanta. Sabo da kamar yadda a kan ce, sara da sassaka ba ya hana gamji toho.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai Ya Zargi Bangaren Shari’a Da Cin Hanci Da Rashawa
  • Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
  • An ceto matar da aka yi garkuwa da ita, da kama mutum 2 a Yobe 
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 5 Hukuncin Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano
  • Kotu Ta Yanke Hukunci Wa Mutum 5 Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano
  • Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC
  • Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho
  • ‘Yansanda Sun Kama Matasa 2 Da Ake Zargi Da Satar Mota A Kebbi
  • Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba
  • Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo