Aminiya:
2025-09-18@00:36:03 GMT

El-Rufai ya nemi afuwa ko mu maka shi a kotu — Gidauniyar Ɗahiru Bauchi

Published: 17th, March 2025 GMT

Gidauniyar Sheikh Ɗahiru Bauchi ta buƙaci Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, da ya nemi afuwar ɗaliban malamin bisa abin da ta kira rashin adalci da aka musu.

Idan kuwa bai yi hakan ba kafin ƙarshen watan Ramadan, za su maka shi a kotu.

An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalma

Wannan na ƙunshe ne a wata takarda da gidauniyar ta fitar, wadda Sayyadi Aliyu Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya sanya wa hannu.

A cewar takardar, dole ne El-Rufai ya fito ya yarda da laifinsa sannan ya nemi afuwar gidauniyar, ɗalibanta da jagoranta, Sheikh Ɗahiru Bauchi.

Gidauniyar ta zargi tsohon gwamnan da bayar da umarni ga jami’an tsaro don su kai samame a makarantun tsangayar Sheikh Ɗahiru Bauchi, inda aka kama wasu ɗaliban karatun Alƙur’ani har zuwa gidansa.

Har yanzu, akwai ɗaliban da ba a san inda suke ba.

Sayyadi ya bayyana cewa an yi hakan ne da gangan domin a tozarta Sheikh Ɗahiru Bauchi da kuma hana ci gaban ilimin addini da ya ke yi.

Ya ce idan har El-Rufai bai nemi afuwa ba kafin ƙarshen Ramadan, za su kai ƙararsa ga Shugaban Ƙasa, ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam, da kotu.

Idan kuwa duka ba su yi musu adalci ba, za su mika ƙarar ga Allah ta hanyar addu’a.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gidauniya Neman Afuwa Sheikh Ɗahiru Bauchi Sheikh Ɗahiru Bauchi

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin

Hukumar jin daɗin jama’a ta Jihar Kwara tare da haɗin gwiwar Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya sun kama wasu mabarata a titunan Ilorin, ciki har da wasu da aka samu da kuɗaɗen ƙasashen waje.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani mabaraci mai suna Musa Mahmud daga Jihar Kano, wanda aka samu da takardar daloli.

Musa Mahmud ya shaida wa manema labarai cewa wani ne ya ba shi takardar Dala a Abuja.

Jami’ai sun bayyana damuwa kan yadda masu bara ke riƙe da kuɗaɗen da ba su dace da yanayin rayuwarsu ba.

Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II

“Za mu bincika asalin waɗannan kuɗaɗen da kuma dalilin da ya sa suke da su,” in ji Adebayo Okunola, shugaban cibiyar gyaran hali a Jihar Kwara.

Jami’an gwamnati sun kwashe kusan mutane 40 daga wuraren da suka haɗa da Tipper Garage, Offa Garage, Tank da Geri Alimi Roundabout.

Jami’an sun ce bakwai daga cikin waɗanda aka kama an taɓa kama su a baya, amma sun koma tituna bayan an sako su.

Kwamishinar jin daɗin jama’a ta jihar, Dakta Mariam Imam, ta ce adadin masu bara da aka kama ya ragu sosai idan aka kwatanta da na baya, inda ta ce suna sauya dabaru don su guje wa kama.

Ta roƙi jama’a da su daina ba wa masu bara kuɗi kai tsaye, su maida gudummawarsu ta hanyar wuraren  ibada da gidajen marayu.

Jami’an gyaran hali sun ce za a tilasta wa waɗanda aka kama su yi aikin tsaftace tituna a matsayin horo da kuma darasi.

Wasu daga cikin masu barar sun roƙi gwamnati da ta tausaya musu, ba su da wata hanyar rayuwa sai bara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin