El-Rufai ya nemi afuwa ko mu maka shi a kotu — Gidauniyar Ɗahiru Bauchi
Published: 17th, March 2025 GMT
Gidauniyar Sheikh Ɗahiru Bauchi ta buƙaci Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, da ya nemi afuwar ɗaliban malamin bisa abin da ta kira rashin adalci da aka musu.
Idan kuwa bai yi hakan ba kafin ƙarshen watan Ramadan, za su maka shi a kotu.
An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalmaWannan na ƙunshe ne a wata takarda da gidauniyar ta fitar, wadda Sayyadi Aliyu Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya sanya wa hannu.
A cewar takardar, dole ne El-Rufai ya fito ya yarda da laifinsa sannan ya nemi afuwar gidauniyar, ɗalibanta da jagoranta, Sheikh Ɗahiru Bauchi.
Gidauniyar ta zargi tsohon gwamnan da bayar da umarni ga jami’an tsaro don su kai samame a makarantun tsangayar Sheikh Ɗahiru Bauchi, inda aka kama wasu ɗaliban karatun Alƙur’ani har zuwa gidansa.
Har yanzu, akwai ɗaliban da ba a san inda suke ba.
Sayyadi ya bayyana cewa an yi hakan ne da gangan domin a tozarta Sheikh Ɗahiru Bauchi da kuma hana ci gaban ilimin addini da ya ke yi.
Ya ce idan har El-Rufai bai nemi afuwa ba kafin ƙarshen Ramadan, za su kai ƙararsa ga Shugaban Ƙasa, ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam, da kotu.
Idan kuwa duka ba su yi musu adalci ba, za su mika ƙarar ga Allah ta hanyar addu’a.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gidauniya Neman Afuwa Sheikh Ɗahiru Bauchi Sheikh Ɗahiru Bauchi
এছাড়াও পড়ুন:
Sheikh Kassim: Mayakan Hizbullah Mazajen Fagen Daga Ne
Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’ima Kassim ya bayyana cewa; Dakarun Hizbullah mazajen fagen daga ne da ba su karbar kankanci.
Sheikh Na’im Kassim wanda ya gabatar da jawabi a wurin babban taron Ashura a ungiyar Dhahiya dake birnin Beirut, ya bayyana cew; Yaki na tsaron kasa zai ci gaba saboda mun yi Imani da ‘yanto da kasa, kuma wajibi ne akansu, ko da kuwa an dauki lokaci mai tsawo sannan kuma sadaukar da kai ya yawaita.”
Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Isra’ila abokiyar gaba tana ci gaba da mamaye yankuna 5 na Lebanon, don haka babu yadda za a yi mu mika kai.” Haka nan kuma ya yi tambayar cewa; Ta yaya za a tsammaci za mu ki tsayuwar daka a gaban wannan abokin gfabar wanda yake ci gaba da mamaye kasa da kuma kisa?
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa; gwagwarmaya za ta ci gaba, kuma zuriya mai zuwa za su dora daga inda aka tsaya.”
Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce: Za mu kare gwagwarmayar da mutane masu yawa su ka sadaukar da kawunansu akanta, domin wannan gwagwarmaya ce ta Imam Musa Assadar, kuma ta Sayyid Hassan Nasrallah shugaban shahidan wannan al’umma.”
Da yake Magana akan yadda HKI take keta wutar yaki, Sheikh Na’im Kassim ya ce; yawan keta wutar yakin Isra’ila ya kai dubban gomomi, ya kuma kara da cewa; Batun da ake yi na wata sabuwar yarjejeniya ba zai sa mu mika wuya ba, abinda ya kamata shi ne a fada wa abokan gaba cewa; Su daina keta wutar yaki, sannan kuma gwgawarmaya tana cikin hanyoyin magance matsalar da ake fuskanta.”