Noman rake: Najeriya da China sun kulla yarjejeniyar kasuwancin $1bn
Published: 15th, April 2025 GMT
Hukumar Bunƙasa Noman Sukari a Najeriya (NSDC) ta sanya hannu kan yarjejeniyar Dala biliyan guda da kamfanin SINOMACH na ƙasar China kan bunƙasa noman rake da sarrafa shi da nufin samar da sukari da kudina ya kai metrik ton miliyan guda.
Kulla yarjejeniyar wani ɓangare ne na shirin Kawancen Najeriya da China, na Gwmanatin Shugaba Bola Tinubu, da nufin kawo masu zuba jari na kimanin Dala biliyan guda a ɓangaren sukari a Najeriya.
Daga cikin yarjejeniyar, Kamfanin SINOMACH zai kafa masana’antar sukari da kuma gonar rake da za su fara da samar da metrik ton 100,000 na sukari a duk shekara.
Kamfanin zai kuma taimaka da kwarewarsa da kayayyakin aikinsa wajen zartar da abubuwan da suka danganci gine-gine sayayyan kayan aiki da ayyukan injiniyarin. Uwa uba, zai samar da kudaden ayyukan.
Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a FilatoA gefe guda kuma Hukumar NSDC za ta taimaka wajen samar da duk takardu da kuma sahalewar gwamnati da ake bukata domin fara aiki.
Da yake jawabi a taron sanya hannun a Abuja, Shugaban Hukumar, Kamal Bakrim ya bayyana cewa shekarar 2025 za ta kasance kashin baya ga samun bunkasar Najeriya.
“Shekara ce da muke sa ran samun gagarumar ci-gaba musamman a fannin tattalin arzikin da samar da wadataccena abinci a kasarmu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Noman rake sukari
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC
Jam’iyyar ADC ta zargin Fadar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinuba da shirya mana wata kutungwila mai hadarin gaske domin kawo cikas ga hadakar ’yan adawan da ke kara samun farin jini.
Sakataren Yada Labarai na ADC na Kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya ce a sakamakon haka gwamnatin APC a matakin kasa ta kira wani taron sirri tsakanin wasu manyan jami’an gwamnati da shugabbanin jam’iyyar ADC na jihohi da kuma kusoshinta daga yankin Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas.
Bolaji Abdullahi ya ce, “muna da sahihan bayanan sirri cewa manufar taron ita ce domin razanawa da tursasa wadannan shugabannin jam’iyar su shirya wa ’yan adawar makarkashiya. Wannan ba siyasa ba ce, tsurku ce.”Ya ci gaba da cewa, hadafin taron na su shi ne “kawo rudani a jam’iyyarmu, bayyana shugabanninta a matsayin haramtattu da kum kawar da ita daga manufofin da ta sanya a gaba, lura da karuwar yadda jam’iyyar take kara samun farin jini a tsakanin ’yan Najeriya
“Wannan shirin na karkatar da hankalin ciyamomin ADC na jihohi da jami’an gwamnati da ya kamata su mayar da hankali kan warware matsalar tsaron da saurannsu da suka addabi kasa, suke yi, ba komai ba ne face hari ga tsarin dimokuradiyya.“Daga haka ake fara samun kasa mai tsarin jam’iyya daya—ta hanyar barazaa,” in ji jami’in na ADC.
Ya ci gaba da cewa, “Hadar ADC ta rikita APC kuma yanzu ta bayyana cewa Gwamnatin Tiubu wadda ta rasu goyon bayan ’yan Najeriya ba za ta iya jure matsin da take ciki a sakamakon wannan hadaka da nagarta ba.“Amma kuma a maimakon ta gyara kurakurenta sai ta kare da kokarin amfani da tsohuwar dabararta ta kawo rudani a jam’iyyun adawa.”
Bolaji Abdullahi ya ce jam’iyyar ta ’yan Najeriya ce, wadanda suka gaji da karairayi da yaudara da kuncin rayuwa. Ta ’yan Najeriya ne masu burin dawo da martaba da kyakkyawan fata da kuma adalci a shugabanci. “Saboda haka ba za mu bar wasu tsirarun mutane masu kama-karya su mayar da kasar nan mai jam’iayya daya ba. Hallo kane a kan kowannenmu ya yaƙi hakan ta yadda ya kamata.”