Aminiya:
2025-10-16@16:51:25 GMT

Kwankwaso ba zai yi mana takara a 2027 ba — NNPP

Published: 5th, July 2025 GMT

Jam’iyyar NNPP, ta bayyana cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya yi mata takarar shugaban ƙasa a 2023, ba zai tsaya takara a 2027 ba.

Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Dokta Agbo Major, ne ya bayyana haka a wata sanarwa, inda ya mayar da martani kan wata magana da Buba Galadima ya yi.

Tinubu ko ɗansa zai naɗa shugaban INEC, APC sai ta faɗi zaɓen 2027 — Dalung Tsadar rayuwa ta sa ’yan Nijeriya na siyan abincin da ya lalace

Galadima, ya ce har yanzu Kwankwaso yana cikin NNPP kuma zai tsaya takara a 2027.

Galadima ya shaida wa manema labarai cewa: “Babu wani tabbaci da ke nuna cewa Kwankwaso yana shirin komawa APC. Za mu ci gaba da zama a NNPP har lokacin zaɓen 2027 ya zo. Muna kira ga ’yan Najeriya su mara masa baya.”

Amma shugaban NNPP ya musanta hakan, inda ya ce: “Kwankwaso da Galadima tun tuni aka kore su daga jam’iyyar. Ba su da hurumin magana a madadin NNPP ko amfani da ita domin yin takara,” in ji Major.

Ya bayyana cewa tafiyar NNPP da Kwankwasiyya ta ƙare tun bayan zaben shugaban ƙasa na 2023.

“Yarjejeniyarmu da Kwankwasiyya ta ƙare bayan zaɓen 2023. Ba za mu amince Kwankwaso ya dawo ba saboda matsalolin da ya janyo mana ba,” in ji shi.

Dokta Major, ya kuma zargi Kwankwaso da yunƙurin karɓe ragamar jam’iyyar ta ƙarfi da yaji.

“Kwankwaso ya canja tambarin jam’iyya zuwa na Kwankwasiyya ba tare da izini ba, kuma ya jefa mu cikin rikicin shari’u marasa tushe. Sai da aka kai kotu kafin INEC ta dawo da tambarinmu na asali,” in ji shi.

Ya ce Kwankwaso yana fatan sake samun damar tsayawa takara kamar yadda ya yi a 2023, amma hakan ba yiwuwa ba.

“Yana tsammanin zai sake samun tikitin takara kamar yadda ya samu a baya, amma hakan ba zai faru ba,” a cewarsa.

Ya ƙara da cewa: “An kori Kwankwaso da tawagarsa daga jam’iyya, kuma ba za mu karɓe su ba. Sun ci amanar jam’iyya. Ba shi da ƙarfin da zai iya ƙalubalantar Tinubu,“ in ji Major.

Sai dai ya amince cewa Kwankwaso yana da ‘yancin tsayawa takara, amma ya ce bai kamata ya jawo jam’iyyar NNPP rikici ba.

“Muna da masu sha’awar tsayawa takara a 2027, kuma za mu bi doka da tsarin jam’iyya wajen fitar da ɗan takara,” in ji shi.

Ya kuma buƙaci ’yan Najeriya da kada su saurari maganganun ’yan Kwankwasiyya.

“Kwankwaso ya kafa tasa jam’iyyar idan yana da muradin yin takara. NNPP ta wuce wannan matakin, ba za mu mayar da hankali kan rigingimun banza ba,” a cewar Dokta Major.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwankwasiyya Kwankwaso Takara Kwankwaso yana takara a 2027 Kwankwaso ya

এছাড়াও পড়ুন:

Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike

Kotun Babban Majistare da ke Yaba ta bayar da umarnin a tono gawarwakin mutane 10 da gobara ta kashe a ginin Afriland Towers da ke Legas a ranar 16 ga Satumba, 2025, domin a gudanar da bincike a kansu.

Alkalin kotun, Mai shari’a Atinuke Adetunji ce ta bayar da umarnin a ranar Talata bayan ta samu labarin cewa an riga da binne wasu daga cikin waɗanda gobarar ta ritsa da su.

“Mai ƙorafi ya rubuta wa Gwamnatin Jihar Legas don neman izinin tono gawarwakin waɗanda suka mutu, sannan a gudanar da bincike a kansu,” in ji Mai Shari’a Adetunji.

Wannan umarni ya biyo bayan wata wasiƙa daga ofishin babban lauya Femi Falana da aka aike wa Babban Mai Kula da Gawarwaki na Jihar Legas, Mai Shari’a Mojisola Dada, a ranar 29 ga watan Satumba, 2025.

Femi Falana (SAN), ta hannun ofishinsa, ya shigar da ƙorafi ga Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Legas, yana neman a gudanar da binciken gawarwaki don gano musabbabin mutuwar da kuma tabbatar da adalci.

A zaman farko na shari’ar, Mai Shari’a Adetunji ta umurci dukkan ɓangarorin da suka halarta da su gabatar da takardun da suka dace kafin zaman kotun na gaba.

Kotun ta kuma gayyaci hukumomi da kamfanoni da suka haɗa da bankin UBA da Hukumar Tara Haraji ta Tarayya (FIRS), Ma’aikatar Kashe Gobara, Afriland Towers, United Capital, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas (LASEMA), Hukumar Tsaro ta Jihar Legas, da sauran masu ruwa da tsaki.

Adetunji ta ƙara da umartar mai ƙorafi da ya tuntubi iyalan waɗanda suka mutu don gano waɗanda ke da niyyar a tono gawar ’yan uwansu domin a gudanar da binciken gawarwaki.

Ta kuma nemi shaidun gani da ido da su bayyana don bayar da bayani kan abin da ya faru.

Lauya Yahaya Atata daga ofishin Falana ya shaida wa kotu cewa zaman na ranar an shirya shi ne don haɗa dukkan masu ruwa da tsaki da kuma fayyace yadda za a gudanar da binciken gawarwaki.

Sai dai alkalin ta lura cewa lauyoyin ba su shirya sosai ba, kuma ta jaddada cewa binciken ba zai ci gaba ba sai an gabatar da dukkan takardun da ake bukata.

Wani lauya mai wakiltar ɗaya daga cikin waɗanda suka mutu, A. O. Mema, ya shaida wa kotu cewa abokinsa, Peter Ifaranmaye, wanda shi ne manaja a Hukumar Tara Haraji ta Tarayya, an riga da binne shi.

Bayan wannan bayani, alkali Adetunji ta jaddada cewa yin binciken gawarwaki yana da matuƙar muhimmanci.

“Binciken gawarwaki muhimmin abu ne. Ba za mu iya gudanar da bincike ba sai an yi bincike don a gano hakikanin abin da ya faru,” in ji ta.

Kotun ta dage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 26 ga watan Nuwamba, 2025.

Gobarar ta tashi ne a ginin Afriland Towers, wani katafaren ginin kasuwanci da ke titin Broad a unguwar Legas Island, a ranar 16 ga watan Satumba, inda ta kashe akalla mutane 10 tare da jikkata wasu da dama.

Shaidu sun ce gobarar ta fara ne da sassafe, kuma ta bazu cikin ginin da sauri kafin hukumomin kasha gobara su samu damar shawo kanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ka da a ɗora wa Tinubu laifin rikicin da ke faruwa a PDP — Fayose
  • Tinubu na ƙoƙarin mayar da Najeriya mai jam’iyya ɗaya — ADC
  • Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP
  • 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa
  • Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
  • DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?
  • PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai
  • Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026