Aminiya:
2025-07-05@18:11:25 GMT

Kwankwaso ba zai yi mana takara a 2027 ba — NNPP

Published: 5th, July 2025 GMT

Jam’iyyar NNPP, ta bayyana cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya yi mata takarar shugaban ƙasa a 2023, ba zai tsaya takara a 2027 ba.

Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Dokta Agbo Major, ne ya bayyana haka a wata sanarwa, inda ya mayar da martani kan wata magana da Buba Galadima ya yi.

Tinubu ko ɗansa zai naɗa shugaban INEC, APC sai ta faɗi zaɓen 2027 — Dalung Tsadar rayuwa ta sa ’yan Nijeriya na siyan abincin da ya lalace

Galadima, ya ce har yanzu Kwankwaso yana cikin NNPP kuma zai tsaya takara a 2027.

Galadima ya shaida wa manema labarai cewa: “Babu wani tabbaci da ke nuna cewa Kwankwaso yana shirin komawa APC. Za mu ci gaba da zama a NNPP har lokacin zaɓen 2027 ya zo. Muna kira ga ’yan Najeriya su mara masa baya.”

Amma shugaban NNPP ya musanta hakan, inda ya ce: “Kwankwaso da Galadima tun tuni aka kore su daga jam’iyyar. Ba su da hurumin magana a madadin NNPP ko amfani da ita domin yin takara,” in ji Major.

Ya bayyana cewa tafiyar NNPP da Kwankwasiyya ta ƙare tun bayan zaben shugaban ƙasa na 2023.

“Yarjejeniyarmu da Kwankwasiyya ta ƙare bayan zaɓen 2023. Ba za mu amince Kwankwaso ya dawo ba saboda matsalolin da ya janyo mana ba,” in ji shi.

Dokta Major, ya kuma zargi Kwankwaso da yunƙurin karɓe ragamar jam’iyyar ta ƙarfi da yaji.

“Kwankwaso ya canja tambarin jam’iyya zuwa na Kwankwasiyya ba tare da izini ba, kuma ya jefa mu cikin rikicin shari’u marasa tushe. Sai da aka kai kotu kafin INEC ta dawo da tambarinmu na asali,” in ji shi.

Ya ce Kwankwaso yana fatan sake samun damar tsayawa takara kamar yadda ya yi a 2023, amma hakan ba yiwuwa ba.

“Yana tsammanin zai sake samun tikitin takara kamar yadda ya samu a baya, amma hakan ba zai faru ba,” a cewarsa.

Ya ƙara da cewa: “An kori Kwankwaso da tawagarsa daga jam’iyya, kuma ba za mu karɓe su ba. Sun ci amanar jam’iyya. Ba shi da ƙarfin da zai iya ƙalubalantar Tinubu,“ in ji Major.

Sai dai ya amince cewa Kwankwaso yana da ‘yancin tsayawa takara, amma ya ce bai kamata ya jawo jam’iyyar NNPP rikici ba.

“Muna da masu sha’awar tsayawa takara a 2027, kuma za mu bi doka da tsarin jam’iyya wajen fitar da ɗan takara,” in ji shi.

Ya kuma buƙaci ’yan Najeriya da kada su saurari maganganun ’yan Kwankwasiyya.

“Kwankwaso ya kafa tasa jam’iyyar idan yana da muradin yin takara. NNPP ta wuce wannan matakin, ba za mu mayar da hankali kan rigingimun banza ba,” a cewar Dokta Major.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwankwasiyya Kwankwaso Takara Kwankwaso yana takara a 2027 Kwankwaso ya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Majalisar Wakilai bakwai na Akwa Ibom sun koma APC

A ci gaba da sauya sheƙar da ’yan Majalisar Wakilai na Tarayya ke yi a ranar Alhamis wasu mambobi bakwai daga Jihar Akwa Ibom sun sanar da sauya sheƙa zuwa Jam’iyyar APC mai mulki.

Cikin waɗanda suka sauya sheƙa sun haɗa da shida daga Jam’iyyar PDP da kuma ɗaya daga Jam’iyyar YPP.

’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro

Shugaban Majalisar Wakilan Tarayya Tajudeen Abbas ne ya karanta wasiƙunsu na sauya sheƙa a zauren Majalisar a ranar Alhamis yayin zaman majalisar.

’Yan majalisar dai sun yi nuni da ƙara samun rarrabuwar kawuna da rigingimun cikin gida a cikin Jam’iyyar PDP a matsayin dalilin da ya sa suka yanke shawarar ficewa daga jam’iyyar.

Waɗanda suka sauya sheƙa daga PDP sun haɗa da: Paul Ekpo da Unyime Idem da Martins Etim da Okpolu Ukpong Etteh da Uduak Odudoh da Okon Ime Bassey.

Shi ma ɗan Majalisa Emmanuel Ukpong-Udo na Jam’iyyar YPP ya koma APC.

’Yan majalisar dai sun ce rikicin da ya ɓarke a Jam’iyyar PDP a Akwa Ibom da ma ƙasa baki ɗaya ya sa ba su iya wakiltar mazaɓarsu yadda ya kamata.

Ficewar ta zo ne makonni kaɗan bayan gwamnan Jihar Akwa Ibom, Umo Eno ya koma APC.

Da yake mayar da martani game da sauya sheƙar, shugaban marasa rinjaye na majalisar, Kingsley Chinda ya nuna baƙin cikinsa game da ci gaban da aka samu.

Chinda ya ce, iƙirarin rarrabuwar kawuna a cikin Jam’iyyar PDP bai dace ba kuma ya saɓawa doka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ko ɗansa zai naɗa shugaban INEC, APC sai ta faɗi zaɓen 2027 — Dalung
  • Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
  • 2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC
  • Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu
  • ’Yan Majalisar Wakilai bakwai na Akwa Ibom sun koma APC
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar TIinubu – Amaechi
  • Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP
  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC