Aminiya:
2025-07-09@05:33:36 GMT

EFCC ta kama Murja Kunya kan wulaƙanta takardun Naira

Published: 17th, March 2025 GMT

Rahotanni sun bayyana cewa Hukumar EFCC reshen Jihar Kano ta cafke shahararriyar jarumar  nan ’yar TikTok, Murja Ibrahim Kunya.

Bayanai sun ce hukumar mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati ta cafke Murja Kunya bisa zargin wulaƙanta takardar Naira.

NAJERIYA A YAU: Guraben Ayyukan Da Aka Kasa Cikewa A Najeriya El-Rufai ya nemi afuwa ko mu maka shi a kotu — Gidauniyar Ɗahiru Bauchi

Wata majiya daga EFCC ta tabbatar da cewa an kama Murja a ranar Asabar a Kano, kuma ana ci gaba da bincike kan lamarin, a cewar Gidan Rediyon Freedom da ke Kano.

Majiyar hukumar ta ce idan bincike ya kammala, za a gurfanar da ita a kotu domin fuskantar hukunci bisa laifin da ake zarginta da aikatawa.

Rahotanni sun nuna cewa an kama Murja kimanin makonni uku da suka gabata, amma ta tsere daga beli kafin sake kama ta a ranar Asabar ɗin.

Murja Kunya ta yi kaurin suna tun bayan fara amfani da kafafen sada zumunta a matsayin abin barkwanci, kafin daga bisani ta mayar da shi dandalin sana’a.

A tsawon lokaci, ta shahara musamman a TikTok, inda take amfani da sunan “Yagayagamen,” duk da cewa a bayan nan ta jawo ce-ce-ku-ce a kanta.

A bayan nan dai hukumar ta EFCC ta cafke wasu abokan sana’ar Murja ’yan TikTok irinsu Alamin G-Fresh da Ashir Idris kan makamancin wannan zargi na wulaƙanta takardun kuɗi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Murja Ibrahim Kunya

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano

Mummunan lamari ya faru ne a lokacin da wata mota kirar bas ta kasuwanci da wata babbar mota ta yi taho-mu-gama da tare da daukar rayukan mutane 21 a hanyar Zariya zuwa Kano.

 

Hadarin ya afku ne a Kasuwar Dogo, Dakatsale, wanda ya hada da wata motar kasuwanci kirar Toyota Hiace da wata tirela ta DAF.

 

Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ta bayyana cewa, binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa direban motar bas din ya saba ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa, lamarin da ya kai ga yin karo da babbar motar da ke zuwa.

 

Hatsarin ya yi sanadiyar mutuwar fasinjoji 21 nan take, wadanda suka hada da manya maza 19 da manya mata 2, yayin da wasu uku suka samu raunuka, kuma an kai musu daukin gaggawa.

 

Jami’an FRSC tare da sauran kungiyoyin bayar da agajin gaggawa sun isa wurin domin gudanar da aikin ceto tare da kwashe tarkacen motocin, wanda hakan ya baiwa ababen hawa damar ci gaba da amfani da hanyar.

 

Da yake tofa albarkacin bakinsa, Shugaban Rundunar FRSC, Marshal Shehu Mohammed, ya bayyana matukar alhininsa game da asarar rayuka da aka yi, ya kuma jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa.

 

Ya kuma tabbatar da cewa, ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike domin gano cikakken al’amuran da suka faru a hatsarin.

 

 

“Wannan mummunan bala’i kuma wani abin tunawa ne mai raɗaɗi na mummunan sakamakon rashin biyayya ga dokokin hanya,” in ji shi.

 

“Tuƙi gangaci da wuce gona da iri sune manyan abubuwan da ke ba da gudummawa ga irin waɗannan bala’o’in da za a iya gujewa a kan hanyoyinmu.”

 

Rundunar ta Corps Marshal ta bukaci dukkan direbobi musamman masu sana’ar tuki da su bi ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa.

 

Ya kuma jaddada cewa za a kara kaimi wajen tabbatar da tsaro da wayar da kan jama’a domin hana ci gaba da asarar rayuka.

 

Hukumar ta FRSC ta yi kira ga masu amfani da hanyar da su kai rahoton hatsarita hanyar kiran lambar kyauta 122, ko kuma a tuntubi duk wata tawagar sintiri ta FRSC.

 

An ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a asibitin Nasarawa dake Kano, inda ake jiran tantancewa da kuma mikawa iyalansu.

 

Rel/Khadijah Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɓarayin babura a Gombe
  • Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
  • ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
  • Jami’an Leken Asirin “Shabak” Na Isra’ila Sun Kama Nasir Lahham Na Tashar Talabijin din Almayadin
  • Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza
  • Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Jigawa ta Kwace Gurbatattun Kayayyaki na Miliyoyin Naira
  • Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a Jos
  • Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC
  • An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine