Aminiya:
2025-12-13@12:29:55 GMT

EFCC ta kama Murja Kunya kan wulaƙanta takardun Naira

Published: 17th, March 2025 GMT

Rahotanni sun bayyana cewa Hukumar EFCC reshen Jihar Kano ta cafke shahararriyar jarumar  nan ’yar TikTok, Murja Ibrahim Kunya.

Bayanai sun ce hukumar mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati ta cafke Murja Kunya bisa zargin wulaƙanta takardar Naira.

NAJERIYA A YAU: Guraben Ayyukan Da Aka Kasa Cikewa A Najeriya El-Rufai ya nemi afuwa ko mu maka shi a kotu — Gidauniyar Ɗahiru Bauchi

Wata majiya daga EFCC ta tabbatar da cewa an kama Murja a ranar Asabar a Kano, kuma ana ci gaba da bincike kan lamarin, a cewar Gidan Rediyon Freedom da ke Kano.

Majiyar hukumar ta ce idan bincike ya kammala, za a gurfanar da ita a kotu domin fuskantar hukunci bisa laifin da ake zarginta da aikatawa.

Rahotanni sun nuna cewa an kama Murja kimanin makonni uku da suka gabata, amma ta tsere daga beli kafin sake kama ta a ranar Asabar ɗin.

Murja Kunya ta yi kaurin suna tun bayan fara amfani da kafafen sada zumunta a matsayin abin barkwanci, kafin daga bisani ta mayar da shi dandalin sana’a.

A tsawon lokaci, ta shahara musamman a TikTok, inda take amfani da sunan “Yagayagamen,” duk da cewa a bayan nan ta jawo ce-ce-ku-ce a kanta.

A bayan nan dai hukumar ta EFCC ta cafke wasu abokan sana’ar Murja ’yan TikTok irinsu Alamin G-Fresh da Ashir Idris kan makamancin wannan zargi na wulaƙanta takardun kuɗi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano Murja Ibrahim Kunya

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe

Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanninta a Jihar Gombe, inda ta jaddada muhimmancin haɗin kai da farfado da jam’iyyar tun daga matakin ƙananan hukumomi zuwa jiha gabanin zaɓen 2027.

Taron ya halarta bayan zuwan wakilai daga dukkanin ƙananan hukumomin jihar.

Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno

Mambobin jam’iyyar sun yaba da yadda komai ya gudana cikin lumana da tsari, abin da suka ce alama ce ta daidaito a cikin jam’iyyar.

Elder Ambrose Ismail Mairungu ne, ya zama sabon shugaban NNPP na jihar, yayin da Yakubu Adamu Tela, ya zama mataimakinsa.

Abdullahi Ali Mohammed, ya samu kujerar sakataren jiha, sannan Hon. Amatiga Yila Naboth (ACG) ya zama sakataren yaɗa labarai.

Sauran da aka zaɓa sun haɗa da Musa Mohammed Gargajiga (Jagoran Matasa), Hajiya Hauwa Mohammed (Shugabar Mata), da Kabiru Mohammed Puma (Sakataren Tsara Ayyuka).

A jawabin da ya gabatar bayan rantsar da su, Mairungu, ya gode wa ’yan jam’iyyar bisa amincewa da suka nuna gare shi, inda ya bayyana cewa sabbin shugabannin za su yi aiki da adalci da tsari, tare da haɗa kowa domin ci gaban jam’iyyar.

Ya ce za su mayar da hankali wajen gina jam’iyyar daga matakin unguwanni, ƙara yawan mambobi, da ƙarfafa shiga matasa da mata a harkokin jam’iyya.

Wasu masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yaba da sabbin shugabannin, inda suka ce suna da damar gyara jam’iyyar kafin tunkarar babban zaɓe.

Haka kuma, sun yi godiya ga Jagoran NNPP na ƙasa, Rabiu Musa Kwankwaso, bisa tallafi da goyon bayan da ya bai wa taron.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Kotu Ta Umarci EFCC Ta Biya Wani Ƴan Kasuwar Kano Miliyan 5, Ta Nemi Afuwar Su
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara