Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da Ta’addancinta Kan Iran
Published: 5th, July 2025 GMT
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta jaddada cewa Ta’addancin yahudawan sahayoniyya kan Iran laifi ne na yaki da ya zama wajibi duniya ta yi mata hukunci a kai
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i ya yi kira da a dorawa mahukuntan yahudawan sahayoniyya alhakin munanan laifukan da suka aikata a kan al’ummar Iran, musamman a lokacin da ake ci gaba da kai hare-hare a birnin Tehran fadar mulkin kasar da sauran garuruwan kasar ta Iran.
A wani sakon da ya wallafa a dandalin X a yau Asabar, Baqa’i ya ce, “Harin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a asibitoci da kurkukun Evin a ranar 24 ga Yunin wannan shekara ta 2025, wanda ya yi sanadin shahadar fararen hula da ma’aikata da kuma masu shigewa da yawansu ya kai mutane 79, yana cikin laifukan yaki da kuma keta dokar jin kai ta kasa da kasa.”
Ya yi nuni da cewa, harin ya afku ne a daidai lokacin da iyalan fursunonin ke taruwa domin ziyartar ‘yan uwansu, kuma sun makale a karkashin baraguzan ginin inda suka yi shahada sakamakon harin wuce gona da iri na jirgin saman yakin gwamnatin mamayar Isra’ila.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Sojojin kasarsa sun koya wa ‘yan sahayoniyya masu wuce gona da iri babban darasi
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, a jawabin da ya gabatar a taron kolin kungiyar Hadin Gwiwar Tattalin Arziki ta ECO da aka gudanar a kasar Azarbaijan a yau Juma’a, ya jaddada cewa: Sojojin kasar Iran bisa doka mai lamba 51 na yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya sun kare al’ummar Iran da mutuncin kasar da cikakken ikonta a yakin da aka yi a baya-bayan nan, kuma sun koyar da masu wuce gona da iri darasi mai girma da kuma dakile yaduwar yaki a wannan yanki.
A yayin taron koli karo na 17 na kungiyar hadin kan tattalin arziki ta ECO da aka gudanar a yammacin yau Juma’a, Pezeshkian ya yi Allah wadai da harin da gwamnatin ‘yan Sahayoniyya ta kai kan kasar Iran, yana mai cewa: Wannan gwamnatin ta fara ne da keta haddin ka’idoji da dokokin kasa da kasa da suka hada da Mataki na 2 sakin layi na 4 na Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya, sannan yakin ci gaba da taimakon sojojin Amurka masu dauke da dabi’ar zalunci kan Iran.
Shugaban Iran ya kara da cewa: A cikin kwanaki 12 na hare-haren wuce gona da irin, an aiwatar da wasu munanan laifuka zalunci kan sojojin da ba sa kan aikinsu da malaman jami’a da talakawan kasa da cibiyoyin makamashin nukiliya na zaman lafiya da suke karkashin kulawar hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa, da kuma kayayyakin more rayuwa.”
Haka nan kuma yayin da yake ishara da irin dimbin hasarar rayukan bil’adama da zaluncin yahudawan sahayoniyya ya janyo kan al’ummar Iran, shugaban ya ce: A bisa ka’ida ta 51 na kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya, sojojin kasar Iran sun taka rawa wajen kare halaltacciyar kasar Iran, ikon da amincin kasa, da cikakken ‘yancin kasa tare da koyar da maharan darasi mai tsauri, da kuma hana yaduwar wannan yanki a yankin.