Ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta bayyana ayyana dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, kuma ta kashe biliyoyin Naira wajen gyara da sabunta makarantun kwana, inda ta ce “nan ba da jimawa ba za a sake buɗe su don yara mata su ci gaba da samun ilimi.”

Ta kuma ƙara da cewa wasu daga cikin makarantun da ke aiki kamar WTC Kano da GGS Dala na karɓar yara daga yankunan da ke kewaye da su, kuma za a yi amfani da irin wannan tsari a sauran makarantun da za a sake buɗewa.

Hajiya Amina ta ƙara da cewa ofishinta ya samu amincewa daga ma’aikatar don gudanar da bincike a wasu yankuna da ke fama da yawan yara mata da ba sa zuwa makaranta ko kuma waɗanda suka daina karatu, don gano matsalolinsu da kawo mafita.

A nasa ɓangaren, Abdulaziz Musa, wanda shi ne mai kula da shirin “Bridging Access to Girls Education” na BCAI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce tattauna ci gaba da ƙalubale da kuma amfani da kuɗaɗen da aka ware don ilimin ’yan mata tare da wakilan gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ’yan jarida.

Ya ce duk da ci gaban da aka samu, har yanzu akwai ƙalubale mai yawa, don haka akwai buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin ciyar da harkar gaba.

Ya ƙara da cewa sun samar da wani tsarin kasafin kuɗi da ya dace da buƙatun mata wanda gwamnati za ta iya amfani da shi wajen tsara yadda za a kashe kuɗin da aka ware don inganta ilimin yara mata a Jihar Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

An kama miji da mata kan zargin mallakar buhuna 360 na Tabar Wiwi

Rahotanni na cewa an kama wani mutum, Onun Ikoli, tare da matarsa, Itam Onun, bisa zargin mallakar buhuna 360 na tabar wiwi a Jihar Kuros Riba.

Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) ce ta cafke ma’auratan a ranar Talata a ƙaramar hukumar Yakurr a jihar ta Kuros Riba.

Osimhen ba zai halarci bikin karrama gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na bana ba Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa

Kwamandan NDLEA na jihar, John Anteyi, yayin zantawarsa da Aminiya a Kalaba, ya ce ababen zargin sun yi iƙirarin cewa tabar wiwin wadda nauyinta ya kai tan 4.706, ta wani mutum ce da suke zaman haya a daya daga cikin dakunan gidansa.

Ma’auratan sun shaida wa ’yan sandan cewa ba su da masaniyar harkar da mutumin yake yi wanda ba a samu nasarar cafke shi ba a gidan.

Itam Onun, mai kimanin shekara 52, ta musanta cewa tabar wiwin ta su ce, inda ta ce: “Ba mu san komai ba. Shi ne mai gidan.

“Mu dai haya muka karɓa a wurinsa kan naira dubu 50, ba mu san irin wannan harkar yake yi ba. Shi ya kawo kayansa ya ajiye amma ga shi an kama mu kan wannan zargin.”

Kwamandan ya ce kawo yanzu dai hukumar tana ci gaba da bincike domin gano ainihin mallakin kayan.

Kazalika, Anteyi ya jaddada cewa wannan samame na cikin yunƙurin da shugaban hukumar NDLEA na ƙasa, Birgediya Janar Buba Marwa (mai ritaya), ke jagoranta na yaƙar miyagun ƙwayoyi da masu safarar su a fadin ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • An kama Faston da ake zargi da yi wa mambobin cocinsa 3 fyade
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai da Malamai a Jihar Neja
  • UNICEF Ta Jinjinawa Jihohin Kano, Katsina da Jigawa Bisa Inganta Rayuwar Kananan Yara
  • Dalibai a Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Koka Game da Ƙalubalen Tsaro a Yankin
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 
  • Nigeria: An Rufe Makarantun Kwana A Jahar Kwara Saboda Matsalar Tsaro
  • An kama miji da mata kan zargin mallakar buhuna 360 na Tabar Wiwi
  • Cibiyar fasaha ta kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin ’yan kasuwa mata a Jihohi 3
  • DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace