Ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta bayyana ayyana dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, kuma ta kashe biliyoyin Naira wajen gyara da sabunta makarantun kwana, inda ta ce “nan ba da jimawa ba za a sake buɗe su don yara mata su ci gaba da samun ilimi.”

Ta kuma ƙara da cewa wasu daga cikin makarantun da ke aiki kamar WTC Kano da GGS Dala na karɓar yara daga yankunan da ke kewaye da su, kuma za a yi amfani da irin wannan tsari a sauran makarantun da za a sake buɗewa.

Hajiya Amina ta ƙara da cewa ofishinta ya samu amincewa daga ma’aikatar don gudanar da bincike a wasu yankuna da ke fama da yawan yara mata da ba sa zuwa makaranta ko kuma waɗanda suka daina karatu, don gano matsalolinsu da kawo mafita.

A nasa ɓangaren, Abdulaziz Musa, wanda shi ne mai kula da shirin “Bridging Access to Girls Education” na BCAI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce tattauna ci gaba da ƙalubale da kuma amfani da kuɗaɗen da aka ware don ilimin ’yan mata tare da wakilan gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ’yan jarida.

Ya ce duk da ci gaban da aka samu, har yanzu akwai ƙalubale mai yawa, don haka akwai buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin ciyar da harkar gaba.

Ya ƙara da cewa sun samar da wani tsarin kasafin kuɗi da ya dace da buƙatun mata wanda gwamnati za ta iya amfani da shi wajen tsara yadda za a kashe kuɗin da aka ware don inganta ilimin yara mata a Jihar Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya sake aike wa Majalisar Dattawa ƙarin sunayen mutum 32 domin tantance su a matsayin jakadu.

Sunayen sun haɗa da manyan mutane kamar tsohon shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Femi Fani-Kayode, da Reno Omokri.

Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe

An raba sunayen zuwa kashi biyu; na farko yana ɗauke da sunan mutum 15 waɗanda suke da gogewar aikin jakadanci da kuma waɗanda ba su gogewar aikin jakadanci mutim 17.

Wasu daga cikin fitattu da suka shiga jerin sun haɗa da tsofaffin gwamnonin kamar Ifeanyi Ugwuanyi da Victor Okezie Ikpeazu, matan tsofaffin gwamnoni kamar Angela Adebayo da Florence Ajimobi, da kuma Sanata Jimoh Ibrahim.

Bayan tantancewa, za a tura jakadun zuwa ƙasashe irin su China, Indiya, Kanada, UAE, Afrika ta Kudu, da Kenya.

Sauran wuraren sun haɗa da manyan cibiyoyi na ƙasa da ƙasa kamar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), UNESCO, da Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU).

Za a bayyana inda za a tura kowane, bayan Majalisar Dattawa ta tantance su.

A makon da ya gabata ne, Tinubu ya tura sunayen mutum uku da ake sa ran tura su Amurka, Birtaniya ko Faransa.

Shugaban ya ce za a sake fitar da ƙarin sunayen jakadu nan ba da jimawa ba.

Wannan mataki na cikin shirin Tinubu na karfafa hulɗar diflomasiyya ta hannun ƙwararru da gogaggun mutane don wakiltar Najeriya a ƙasashen waje.

Ana sa ran Majalisar Dattawa za ta fara tantance su cikin makonni masu zuwa, kafin su kama aiki.

Masu sharhi kan sha’anin siyasa suna ganin waɗanda aka zaɓo ƙwararru ne kuma za su taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasar gida da waje.

Da dama na ganin cewa waɗannan naɗe-naɗen za su iya taka rawa wajen tsara sabuwar hanyar hulɗa da ƙasashen waje da manufofin diflomasiyyar Najeriya a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno
  • Najeriya :  Sojoji sun kubutar da yan mata 12 da mayakan ISWAP
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
  • Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba
  • Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Yadda ’yan mata ke kufancewa da kasuwancin fara a Kano