Ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta bayyana ayyana dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, kuma ta kashe biliyoyin Naira wajen gyara da sabunta makarantun kwana, inda ta ce “nan ba da jimawa ba za a sake buɗe su don yara mata su ci gaba da samun ilimi.”

Ta kuma ƙara da cewa wasu daga cikin makarantun da ke aiki kamar WTC Kano da GGS Dala na karɓar yara daga yankunan da ke kewaye da su, kuma za a yi amfani da irin wannan tsari a sauran makarantun da za a sake buɗewa.

Hajiya Amina ta ƙara da cewa ofishinta ya samu amincewa daga ma’aikatar don gudanar da bincike a wasu yankuna da ke fama da yawan yara mata da ba sa zuwa makaranta ko kuma waɗanda suka daina karatu, don gano matsalolinsu da kawo mafita.

A nasa ɓangaren, Abdulaziz Musa, wanda shi ne mai kula da shirin “Bridging Access to Girls Education” na BCAI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce tattauna ci gaba da ƙalubale da kuma amfani da kuɗaɗen da aka ware don ilimin ’yan mata tare da wakilan gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ’yan jarida.

Ya ce duk da ci gaban da aka samu, har yanzu akwai ƙalubale mai yawa, don haka akwai buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin ciyar da harkar gaba.

Ya ƙara da cewa sun samar da wani tsarin kasafin kuɗi da ya dace da buƙatun mata wanda gwamnati za ta iya amfani da shi wajen tsara yadda za a kashe kuɗin da aka ware don inganta ilimin yara mata a Jihar Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa har yanzu yana nan daram a jam’iyyar PDP.

Ya yi wannan bayani ne a Abuja a ranar Juma’a yayin da yake mayar da martani kan ficewar wasu ’yan majalisar dokoki na Jihar Rivers daga PDP zuwa jam’iyyar APC.

Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15

A ranar Juma’a, ‘yan majalisar Ribas guda 16, ciki har da Kakakin Majalisar, Martins Amaewhule, da suka sauya sheƙa zuwa APC.

Amaewhule, ya ce ya yanke shawarar komawa APC ne saboda rarrabuwar kai da aka samu a PDP.

Hakazalika, kakakin ya ce yana son ya yi aiki tare da Shugaba Bola Tinubu, bayan ya gano yana da kyakkyawan tsari na ciyar da ƙasar nan gaba.

Da yake magana da manema labarai bayan duba wasu ayyuka a Abuja, Wike, ya ce ’yan majalisun ba su tuntuɓe shi game da batun sauya sheƙarsu ba, amma ya ce suna da  ’yancin zaɓen abin da suke so.

Ya ƙara da cewa ba duka ’yan majalisar ne suka fice daga PDP ba.

Ya ce, “Ni har yanzu ina PDP. Ba dukkaninsu ne suka fice daga jam’iyyar PDP ba. Ina ganin 16 ko 17 ne suka fice daga cikin 27. Har yanzu muna da kusan mutum 10, kuma za mu ci gaba da aiki tare da su.”

Wike, ya bayyana lamarin a matsayin abin baƙin ciki, amma ya ce kowa na da ’yancin zaɓen abin da yake so.

Ya ɗora alhakin ficewarsu kan rikicin cikin gida da PDP ke fama da shi, inda ya bayyana cewa kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya bai wa mutane damar barin jam’iyyar idan ta rabu gida biyu.

Ya ce tun da farko ya bai wa shugabancin PDP shawara su gyara jam’iyyar, tare da gargaɗin cewa idan ba a ɗauki mataki ba jam’iyyar za ta ci gaba da yin asara.

Wike, ya ƙara da cewa suna ci gaba da ƙoƙari domin sauran mambobin PDP su haɗa kai don yaƙar jam’iyyun adawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata
  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • Jagora: Musulunci Ya Daukaka Mata Matukar Dauka
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina