Ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta bayyana ayyana dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, kuma ta kashe biliyoyin Naira wajen gyara da sabunta makarantun kwana, inda ta ce “nan ba da jimawa ba za a sake buɗe su don yara mata su ci gaba da samun ilimi.”

Ta kuma ƙara da cewa wasu daga cikin makarantun da ke aiki kamar WTC Kano da GGS Dala na karɓar yara daga yankunan da ke kewaye da su, kuma za a yi amfani da irin wannan tsari a sauran makarantun da za a sake buɗewa.

Hajiya Amina ta ƙara da cewa ofishinta ya samu amincewa daga ma’aikatar don gudanar da bincike a wasu yankuna da ke fama da yawan yara mata da ba sa zuwa makaranta ko kuma waɗanda suka daina karatu, don gano matsalolinsu da kawo mafita.

A nasa ɓangaren, Abdulaziz Musa, wanda shi ne mai kula da shirin “Bridging Access to Girls Education” na BCAI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce tattauna ci gaba da ƙalubale da kuma amfani da kuɗaɗen da aka ware don ilimin ’yan mata tare da wakilan gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ’yan jarida.

Ya ce duk da ci gaban da aka samu, har yanzu akwai ƙalubale mai yawa, don haka akwai buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin ciyar da harkar gaba.

Ya ƙara da cewa sun samar da wani tsarin kasafin kuɗi da ya dace da buƙatun mata wanda gwamnati za ta iya amfani da shi wajen tsara yadda za a kashe kuɗin da aka ware don inganta ilimin yara mata a Jihar Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 

Maiyaki ya ce, “Gwamna Uba Sani kwanan nan ya ba da izinin daukar ma’aikatan lafiya 1,800 nan take a karkashin rukunoni daban-daban.

 

“Za a ci gaba da yin hakan a cikin shekaru biyar masu zuwa, da nufin inganta harkar lafiya a jihar.”

 

Maiyaki ya ci gaba da cewa, Gwamna Sani ya fifita harkar kiwon lafiya a gwamnatinsa, inda take gaba-gaba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5 November 10, 2025 Labarai Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta  November 10, 2025 Labarai Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC November 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Ɗauki Ma’aikatan Lafiya 9,000 Cikin Shekaru 5 – Maiyaki 
  • Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5
  • ’Yan bindiga sun sace mata 5 a Kano
  • NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
  • Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura
  • Uwargidan Gwamnan Gombe ta nemi a tsawaita hutun haihuwa na mata ma’aikata
  • Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko
  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan
  • An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai