Ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta bayyana ayyana dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, kuma ta kashe biliyoyin Naira wajen gyara da sabunta makarantun kwana, inda ta ce “nan ba da jimawa ba za a sake buɗe su don yara mata su ci gaba da samun ilimi.”

Ta kuma ƙara da cewa wasu daga cikin makarantun da ke aiki kamar WTC Kano da GGS Dala na karɓar yara daga yankunan da ke kewaye da su, kuma za a yi amfani da irin wannan tsari a sauran makarantun da za a sake buɗewa.

Hajiya Amina ta ƙara da cewa ofishinta ya samu amincewa daga ma’aikatar don gudanar da bincike a wasu yankuna da ke fama da yawan yara mata da ba sa zuwa makaranta ko kuma waɗanda suka daina karatu, don gano matsalolinsu da kawo mafita.

A nasa ɓangaren, Abdulaziz Musa, wanda shi ne mai kula da shirin “Bridging Access to Girls Education” na BCAI, ya bayyana cewa manufar taron ita ce tattauna ci gaba da ƙalubale da kuma amfani da kuɗaɗen da aka ware don ilimin ’yan mata tare da wakilan gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, da kuma ’yan jarida.

Ya ce duk da ci gaban da aka samu, har yanzu akwai ƙalubale mai yawa, don haka akwai buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da ƙungiyoyi masu zaman kansu domin ciyar da harkar gaba.

Ya ƙara da cewa sun samar da wani tsarin kasafin kuɗi da ya dace da buƙatun mata wanda gwamnati za ta iya amfani da shi wajen tsara yadda za a kashe kuɗin da aka ware don inganta ilimin yara mata a Jihar Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano

’Yan sanda sun kama tsohon Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), Muhuyi Magaji Rimin Gado.

Rahotanni sun nuna cewar wasu ’yan sanda ɗauke makamai ne suka kama shi a ofishinsa da ke Kano, bayan tafka jayayya a ranar Juma’a.

Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026 Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum

Waɗanda lamarin ya faru a kan idonsu, sun  ce manyan motocin ’yan sanda cike da jami’an da ke ɗauke da makamai ne suka dira ofishinsa da ke kan titin zuwa Zariya.

Sun gargaɗi mutane da kada kowa ya kusanci ofishin, inda suka yi barazanar buɗe wa duk wanda ya yi yunƙurin tsoma baki a lamarin wuta.

Muhuyi, ya nemi jami’an su nuna masa takardar kama shi ko su bayyana dalilin kama shi.

Sai dai jami’an sun ƙi bayyana komai, face cewar umarni aka ba su daga Hedikwatar ’Yan Sanda ta Ƙasa da ke Abuja.

Lauya Ridwan Zakariyya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce bayan tafka jayayya, daga bisani an kai Muhuyi hedikwatar ’yan sanda ta Kano da ke Bompai.

Ya ce jami’an sun ce su wani rukuni ne na musamman na Sufeto Janar na ’Yan Sanda da aka aiko daga Abuja.

Zakariyya, ya ƙara da cewa jami’an sun yi yunƙurin ƙwace wayar Muhuyi tare da yin barazanar harbi.

Wannan shi ne karo na biyu da ake kama Muhuyi a shekarar 2025.

A farkon watan Janairu, rundunar IGP Monitoring Unit ta kama shi kan almundahanar wasu kuɗaɗe da ake zargin suna da alaƙa da wani jigo na jam’iyyar APC, amma daga baya aka sake shi.

Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Kano, CSP Abdullahi Kiyawa, ya ci tura, domin bai amsa wayarsa ba, zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Mata ‘yar wasan harbi ta Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya a karo na 4
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya