HausaTv:
2025-11-02@21:16:47 GMT

Trump na shan martani game da harajin da ya laftawa kasashen duniya

Published: 4th, April 2025 GMT

Kasashen duniya na ci gaba da mayar da martini tare da shan alwashin ramuwar gayya game da harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya lafta musu kankan kayayyakin da ake shigowa da su kasar.

 Gwamnatoci da kamfanoni da dama sun sanar da matakan gaggawa na samar da matakan dakile matakin da Amurkan ta dauka kansu.

A ranar Laraba ne, ya sanya harajin kan duk kayayyakin da ake shigowa da su Amurka da kuma karin haraji kan wasu manyan abokan kasuwancin kasar.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi kira ga kamfanonin Turai da su dakatar da shirin zuba jari a Amurka.

“Ina ganin abin da ke da muhimmanci, shi ne a dakatar da saka hannun jarin da za a cikin ‘yan makonnin nan har sai an fayyace al’amura da Amurka,” in ji Macron yayin ganawarsa da wakilan masana’antun Faransa.

Kasar China ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya ta sha alwashin daukar fansa kan harajin kashi 54% na Trump kan shigo da kaya.

Hakazalika, Tarayyar Turai ta sanar da cewa za ta bullo da matakan da za su bijirewa aikin da Amurka ke yi na kashi 20%.,” in ji shugabar EU Ursula von der Leyen.

Koriya ta Kudu, Mexico, Indiya, da sauran abokan cinikin Amurka da yawa sun ce za su daina aiki a yanzu yayin da suke neman rangwame kafin harajin da aka yi niyya ya fara aiki a ranar 9 ga Afrilu.

Jami’an Mexico sun ce za su ci gaba da tattaunawa da gwamnatin Trump, yayin da

Canada ta ce tana bukatar yin garambawul ga tattalin arzikinta domin rage dogaro da Amurka, ta kuma sha alwashin mayar da martani kan harajin da Trump ya saka mata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara November 2, 2025 Wasanni Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar? November 2, 2025 Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare