HausaTv:
2025-04-30@19:23:34 GMT

Trump na shan martani game da harajin da ya laftawa kasashen duniya

Published: 4th, April 2025 GMT

Kasashen duniya na ci gaba da mayar da martini tare da shan alwashin ramuwar gayya game da harajin da shugaban Amurka Donald Trump ya lafta musu kankan kayayyakin da ake shigowa da su kasar.

 Gwamnatoci da kamfanoni da dama sun sanar da matakan gaggawa na samar da matakan dakile matakin da Amurkan ta dauka kansu.

A ranar Laraba ne, ya sanya harajin kan duk kayayyakin da ake shigowa da su Amurka da kuma karin haraji kan wasu manyan abokan kasuwancin kasar.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi kira ga kamfanonin Turai da su dakatar da shirin zuba jari a Amurka.

“Ina ganin abin da ke da muhimmanci, shi ne a dakatar da saka hannun jarin da za a cikin ‘yan makonnin nan har sai an fayyace al’amura da Amurka,” in ji Macron yayin ganawarsa da wakilan masana’antun Faransa.

Kasar China ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya ta sha alwashin daukar fansa kan harajin kashi 54% na Trump kan shigo da kaya.

Hakazalika, Tarayyar Turai ta sanar da cewa za ta bullo da matakan da za su bijirewa aikin da Amurka ke yi na kashi 20%.,” in ji shugabar EU Ursula von der Leyen.

Koriya ta Kudu, Mexico, Indiya, da sauran abokan cinikin Amurka da yawa sun ce za su daina aiki a yanzu yayin da suke neman rangwame kafin harajin da aka yi niyya ya fara aiki a ranar 9 ga Afrilu.

Jami’an Mexico sun ce za su ci gaba da tattaunawa da gwamnatin Trump, yayin da

Canada ta ce tana bukatar yin garambawul ga tattalin arzikinta domin rage dogaro da Amurka, ta kuma sha alwashin mayar da martani kan harajin da Trump ya saka mata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani

Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Duk wani harin wuce gona da iri kan Iran zai fuskanci mayar da martani daidai da shi cikin gaggawa

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa Iran na da kwarin gwiwa kan iya dakile duk wani yunkuri da wasu bangarorin ke yi na kawo cikas ga manufofinta na ketare.

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Rudun gwamnatin yahudawan sahayoniyya, wadda take ganin za ta iya gindaya wa Iran abin da ya kamata ko kuma bai kamata ba, rudun tunani ne da ya yi nesa da hakikanin gaskiya, ta yadda bai cancanci mayar da martani ba.

Araqchi ya kara da cewa: “Duk da haka, jajircewar Netanyahu wani abin lura ne, a yayin da yake kokarin neman bayyana wa Shugaba Trump abin da zai iya ko kuma ba zai iya yi a diflomasiyyarsa da Iran ba!”

Ministan harkokin wajen ya yi nuni da cewa: “Abokanan Netanyahu a cikin tawagar Biden da ta gaza – wadanda suka kitsa makarkashiyar hana cimma yarjejeniya da Iran – suna kokarin nuna zaman tattaunawar da ake yi ba na kai tsaye ba da gwamnatin Trump a matsayin wani kuskure ne kuma tamkar hoton sauran yarjejeniyar nukiliya ce da aka gudanar.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba