Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana yau Alhamis cewa, kasar Sin ta bukaci Amurka da ta gyara kuskuren da ta yi na kakaba “harajin ramuwar gayya,” kana ta magance sabanin dake tsakaninta da kasar Sin da sauran kasashen duniya dangane da tattalin arziki da cinikayya, ta hanyar yin shawarwari bisa daidaito, da mutunta juna ta yadda bangarorin za su ci moriyar juna.

Guo ya bayyana hakan ne a taron manema labarai na yau, a matsayin martani ga wata tambaya game da sanarwar da Washington ya yi na kakaba “harajin ramuwar gayya” kan manyan abokan cinikiayya. Yana mai cewa, a karkashin manufar “ramuwar gayya”, Amurka ta sanya karin harajin fito kan kayayyakin da ake fitarwa daga kasar Sin da sauran kasashe, wanda hakan ya sabawa ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya da matukar yin illa ga tsarin cinikayya tsakanin bangarori daban daban, kana ya nanata cewa, babu wanda zai yi nasara a takaddamar cinikayya ko harajin fito, kuma kariyar cinikayya ba za ta samar da mafita ba.

A wani ci gaban kuma, kakakin ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin He Yadong ya bayyana a taron manema labaru na yau Alhamis cewa, kasar Sin a shirye take ta warware damuwar da ke tsakaninta da Amurka ta hanyar yin shawarwari bisa daidaito da tuntubar juna. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba

Babban hafsan hafsoshin sojan Iran Manjo janar Musawi ya ce, ko kadan Iran ba ta yarda ko gaskata alkawullan Amurka,balle kuma zancen ‘yan sahayoniya.

Babban hafsan hafsoshin sojan na Iran ya kuma kara da cewa, sojojin kasar suna cikin Shirin ko-ta-kwana domin kalubalantar duk wan igigi na abokan gaba.

Manjo janar Musawi ya bayyana hakan ne dai a lokacin da ya yi tattaunawa ta wayar tarho da ministan tsaron kasar Tajikistan Manjo janar  Imam Ali Sabir Zadeh.

A nashi gefen, ministan tsaron kasar ta Tajikistan, ya fara da yi wa janar Musawi murnar zabarsa sabon hafsan hafsoshin sojan kasar ta Iran, sannan kuma ya nuna bakin cikinsa akan rashin kwamandojin sojan Iran da su ka yi shahada a sanadiyyar harin ta’addancin HKI.

Manjo janar Imam Ali Sabir Zadeh ya kuma kara da cewa, al’ummar kasar Tajikinstan sun yi bakin ciki, don haka suna isar da ta’aziyyarsu ga al’ummar Iran.

Har ila yau minstan tsaron kasar ta Tajikistan ya yi ishara da tarayya akan harshe da al’ada da kasashen biyu su ka yi, haka nan kuma tarihi.

Haka nan kuma manjo janar Musawi ya yi wa Tajikistan godiya akan yadda ta kasance a tare da Iran a lokacin yakin kwanaki 12, lamarin da ya kara karfin alakar kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021
  • Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500
  • Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya
  • Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5