Rasha ta gargadi Amurka kan duk wani gigin ka wa kasar Iran hari
Published: 3rd, April 2025 GMT
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Rasha ya gargadi Amurka da cewa. duk wani harin soji a kan cibiyoyin nukiliyar Iran zai haifar da “mummunan sakamako” ga daukacin yankin.
Sergei Ryabkov ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da wata mujallar harkokin kasa da kasa, bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar kai wa Iran hari idan har ta kasa cimma matsaya da Washington kan shirinta na nukiliya.
Ryabkov ya ce, “Hakika ana jin barazanar, ana kuma jin bayanai kan abubuwan da suka dace,” in ji Ryabkov, yana mai cewa “Sakamakon hakan, musamman idan harin ya kasance kan kayayyakin nukiliya, na iya zama bala’i ga daukacin yankin.”
Ya ce sabbin kalaman na Trump za su kara dagula al’amura ne kawai da kuma rikitar da lamurra dangane da sha’anin Iran.
Ya kara da cewa, “Muna daukar irin wadannan hanyoyin da ba su dace ba, a matsayin wata hanya da Amurka ke bi domin cimma muradunta ta hanyoyin da basu dace ba, kuma sun saba wa ka’ida da doka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine
Fadar Kremlin ta kasar Rasha ta ayyana tsagaita wuta na kwana biyu ita kaɗai a yakinta da kasar Ukraine.
Shugaba Vladimir Putin ya sanar a ranar Litinin cewa Rasha za ta aiwatar da tsagaita wutar ne daga tsakar dare na 8 ga Mayu zuwa tsakar dare na 10 ga Mayu.
A ranakun da za a tsagaita wutar ne Rasha ke bikin karshen da yakinta da kasar Jamus a shekarun 1941 zuwa 1945, wanda aka fi sani da Yakin Duniya na Biyu a yawancin duniya.
A Rasha ana kiran yakin na Duniya na biyu da sunan Babban Yaƙin Ceton Kasa.
Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi