Iran ta yi kira ga kungiyar Shanghai ta yi Allah wadai da barazanar Trump
Published: 4th, April 2025 GMT
Jamhuriyar Musulinci ta Iran ta yi kira ga kasashe mambobi kungiyar hadin guiwa ta Shanghai da ta yi Allah wadai da barazanar Trump ta baya baya nan kan kasar.
A taron ministocin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai da aka gudanar a birnin Moscow a ranar Alhamis, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran Majid Takht Ravanchi, ya yi kira ga mambobin kungiyar SCO da su yi Allah wadai da kalaman da shugaban na Amurka Donald Trump ya yi a baya-bayan nan kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, lamarin da ya ce yana da hadari.
Majid Takht Ravanchi ya yi kakkausar suka ga barazanar harin bam da Trump ya yi a wata hira da tashar NBC News, inda ya ce, hakan ya keta dokokin kasa da kasa, da kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya wanda ya haramta amfani da karfi karara a kan iyakokin kasa da ‘yancin kai.
Takht Ravanchi ya bayyana cewa Iran ta bukaci kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya yi Allah wadai da wannan hali da ba za a amince da shi ba tare da daukar matakan da suka dace don kiyaye zaman lafiya da tsaron kasa da kasa.
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya sake jaddada matsayar kasar Iran da cewa duk wani yunkuri daga Amurka zai fuskanci mai da martani cikin gaggawa.
Ya yi kira da a fitar da sanarwar hadin gwiwa ta SCO da ke yin Allah wadai da barazanar Amurka tare da yin kira ga kwamitin sulhun da ya sauke nauyin da ya rataya a wuyansa na wanzar da zaman lafiya da tsaro a duniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yi Allah wadai da
এছাড়াও পড়ুন:
Wulayati: Hanyar Zangezur Wata Shirin Amurka Ne Don Matsa lamba Kan Kasashen Iran Da Rasha
Mai ba da shawara ga Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci ya bayyana cewa: Hanyar Zangezur wata shiri ne na Amurka don matsawa kasashen Rasha da Iran.
Ali Akbar Velayati mai ba wa Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran shawara kan harkokin kasa da kasa, ya dauki aikin Zangezur (arewa maso yammacin Iran) a matsayin wani aikin Amurka na matsawa kasashen Rasha da Iran lamba.
A cikin wani sako na tunawa da Sheikh Safi al-Din Ardebili, Velayati ya yi tsokaci kan batutuwan da suka shafi Azarbaijan da mashigar Zangezur, yana mai cewa, “Makiya Iran karkashin jagorancin ‘yan sahayoniyyan duniya da Amurka, suna neman ta hanyar tsare-tsare irin su mashigar Zangezur, don ciyar da manyan ayyukan siyasa a karkashin fakewa da wadannan tsare-tsare.”
Ya kara da cewa, manufar farko ita ce raunana gwagwarmaya da yanke alakar Iran da yankin Caucasus da kuma killace Iran da Rasha ta kasa a kudancin yankin.
Ya bayyana cewa: “Wannan aikin ba wai kawai wani bangare ne na shirin Amurka na maye gurbin Ukraine da yankin Caucasus a matsayin wani sabon fage na matsin lamba kan Rasha da Iran ba, amma ana aiwatar da shi ne tare da goyon bayan kungiyar tsaro ta NATO da kuma wasu kungiyoyin ‘yan kishin kasa na Turkiyya (Pan-Turkist).