Leadership News Hausa:
2025-10-19@16:27:50 GMT

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Published: 19th, October 2025 GMT

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

 

Abubuwan bukata:

Tafarnuwa, Kanunfari, Kurkum, Citta danya, Kajiji, Kimba, Bagaruwa, Masoro, Aiden fruit, Cinnamon sticks, Lemon tsami, Ruwa Lita 6

 

Yadda za a hada: 

Hade su ake yi a tafasa a rika sha kofi daya safe da yamma na kwanaki bakwai, In sha Allah za a samu lafiya. A kiyaye

Ban da maza marasa aure, Ban da mata masu ciki, Ban da masu Olsar da ta yi tsanani.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Adon Gari Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki? October 12, 2025 Adon Gari Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu? August 31, 2025 Ado Da Kwalliya Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa August 3, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Kafa Dokar Wuraren Tsaro A Makarantu

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta fara aiki kan dokar da za ta kafa wuraren tsaro (safe spaces) a makarantu domin karfafa ilimin yara mata a jihar.

Shugaban Kwamitin Ilimi, Honarabul Mahmud Lawal, ya bayyana hakan a babban taro kan Ilimin Yara Mata  da aka gudanar a Zariya, wanda Cibiyar Kula da Ilimin Yara Mata (CGE) ta shirya don tunawa da Ranar Yara Mata ta Duniya ta 2025.

Ya ce dokar, mai taken “Dokar Wuraren Tsaro a Jihar Kaduna, 2025,” za ta kare ‘yan mata daga cin zarafi, hana wariya, da samar da tsarin horaswa da rahoto a makarantu.

Daraktar CGE, Hajiya Habiba Mohammed, ta ce taron na da nufin kara karfafa ‘yan mata a matsayin shugabannin da za su kawo sauyi, musamman a lokacin rikice-rikice da suke fuskantar kalubale irin su aure da wuri da barin makaranta.

 

Ta ce cibiyarsu na ganin ilimi a matsayin makamin da zai bai wa ‘yan mata damar canza al’umma, kuma dokar majalisar za ta taimaka wajen tabbatar da shirye-shiryen su a makarantu.

A jawabinsa a wurin taron, Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Farfesa Adamu Ahmed, ya yaba da taken taron, yana mai cewa ya dace da kalubalen da ‘yan mata ke fuskanta.

Ya ce daya cikin kowanne ‘yan mata hudu a yankin na yin aure kafin shekaru 18, kuma har yanzu ba su da daidaiton damar ilimi kamar maza.

Farfesa Ahmed ya bayyana cewa ABU na kara yawan ‘yan mata da take karɓa, inda suka kai kashi 42 cikin 100, tare da kira ga gwamnati da masu ruwa da tsaki su kara zuba jari a ilimin ‘yan mata.

 

Ibrahim Suleiman

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Ake Alkaki
  • Yadda ma’aurata 136 sun kashe juna a shekara 4
  • Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
  • Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Kafa Dokar Wuraren Tsaro A Makarantu
  • Jihar Jigawa Ta Dukufa Wajen Gina Magudanan Ruwa Domin Kaucewa Ambaliya
  • Ba mu ji dadin yi wa mahaifinmu afuwa tare da riƙaƙƙun masu laifi ba – Iyalan Herbert Macaulay
  • Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara
  • FMC Birnin Kudu Ya Yi Bikin Ranar Maganin Kashe Radadi Ta Duniya