Leadership News Hausa:
2025-12-03@09:16:17 GMT

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Published: 18th, October 2025 GMT

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

 

Gyaran Gonar Shuka Ta:

Kafin ka shuka Irinta, ana bukatar ka tabbatar da kasar nomanta mai kyau ce.

 

Zaɓo Nau’inta Da Ya Dace:

A nan ana bukatar ka zabo daga cikin nau’ikanta abiyu, wato na Udara ko kuma na Agbalumo, inda ake iya gano su ta hanyar girmansu.

Amfanin na kai wa tsawaon shekara takwas kafin ta kammala girma, inda kuma aka kara habaka nau’insa, wanda zai iya girma bayan shekara uku.

Kazalika, akwai matakan da ake bi wajen yi mata girbi, wacce akasari ana girbe ta ne a watan Disamba.

Ana kuma shuka irinta ne, wanda idan manomi zai sayo Irin nomansa, sai ya tabbatar da ya sayo a gurin da aka fi sani, musamman don ya samu ingantacce kuma mai lafiya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul October 18, 2025 Noma Da Kiwo Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI October 18, 2025 Noma Da Kiwo Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya October 11, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano

’Yan bindiga sun harbe wata tsohuwa har lahira a wani sabon hari da suka kai ƙauyen Yankamaye da ke Ƙaramar Hukumar Tsanyawa a Jihar Kano.

Sun kai harin ne a daren ranar Asabar, a lokacin da mutanen ƙauyen ke kwance.

Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32

Yayin kai harin, ’yan bindigar sun kuma sace aƙalla mutum uku.

Yankamaye, wani ƙaramin ƙauyen manoma ne, ’yan bindiga da ke tserewa daga maƙwabtan jihohin Kano ne suka fara kai musu hare-hare.

Kakakin rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an tura jami’ai domin bin diddigin maharan.

Mazauna ƙauyen sun ce ’yan bindigar sun isa ne a kan babura inda suka ajiye su daga nesa, sannan suka shiga ƙauyen a ƙafa.

A yayin taron majalisar zartarwa da aka gudanar kwanan nan, Gwamna Abba Yusuf, ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na magance matsalar tsaro.

Ya kuma ce hare-haren ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane, da ɓarayi shanu a wasu yankunan Arewacin jihar, babban abin damuwa ne.

Gwamnan, ya ce suna aiki tare da hukumomin tsaro don magance barazanar da kuma tabbatar da zaman lafiya.

Ya bayyana ƙananan hukumomin da abin ya shafa; Kunchi, Tsanyawa, Gwarzo, Kabo, Sumaila, Shanono, Tudun Wada, Doguwa, da Rogo.

Amma ya ce hukumomi na ci gaba da ayyuka domin toshe hanyoyin shigowar ’yan bindiga da kuma kare al’ummomin ƙauyuka.

“Duk da wasu ƙalubale da ake fuskanta a nan da can, jama’a su kwantar da hankalinsu, gwamnati tana aiki domin magance duk wata barazana ga zaman lafiya,” in ji Yusuf.

Gwamnan, ya kuma goyi bayan matakin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, na ayyana dokar ta-ɓaci a harkar tsaro a faɗin ƙasar nan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • Tinubu ya naɗa Janar CG Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano