Aminiya:
2025-10-19@10:51:23 GMT

An kama sojoji 20 kan yunƙurin kifar da gwamnatin Tinubu

Published: 19th, October 2025 GMT

Bayanai daga rundunar sojin Najeriya na cewa an kafa wani kwamiti da ke binciken wasu jami’ai 20 da aka tsare bisa zargin yunƙurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Jaridar Premium Times ta ruwaito wata majiyar soji da ke da masaniya kan lamarin tana cewa al’amarin ya faru ne a ƙarshen watan Satumba.

An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano An tsinci gawar wata mata da aka yi wa kisan gilla a Yobe

Majiyar ta ce ana zargin jami’an da shirya zubar da jini a juyin mulkin, kasancewar akwai sunayen wasu manyan jami’an gwamnati da aka shirya yi wa kisan gilla.

A cewar majiyar kamar yadda Premium Times ta ruwaito, daga cikin manyan jami’an gwamnatin waɗanda masu kitsa juyin mulkin suka shirya yi wa kisan gilla akwai shugaba Bola Tinubu da matamaikinsa, Kashim Shettima da kuma shugabannin Majalisun Tarayya, Sanata Godswill Akpabio da Abbas Tajudeen da sauransu.

Waɗanda ake zargin dai, bayanai sun tabbatar da cewa sun tsayar da ranar da za su kifar da gwamnatin farar hula, yayin da suke tuntuɓar juna a kai a kai.

Wannan yunƙuri na juyin mulkin ya haifar da firgici a tsakanin manyan jami’an gwamnati bayan da aka fallasa shi, duk da cewa babban hafsan sojin ƙasar ya sha ba wa gwamnatin Najeriyar tabbacin goyon bayan sojoji ga gwamnati.

An kuma ruwaito cewa saboda kaɗuwar wannan labari ne, gwamnati ta soke faretin cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ’yancin kai na ranar 1 ga Oktoba, kasancewar bikin sojoji ne ke jan ragamarsa.

Majiyar ta ƙara da cewa, rundunar ta kafa wani kwamitin bincike da zai bibiyi abin da hukumomi suka bayyana a matsayin rashin ɗa’a da kuma saba ƙa’idojin aiki.

Wata majiya ta ce kwamitin ya shafe makon da ya gabata yana zaman bibiyar al’amarin, amma har yanzu ba a san inda aka kwana ba.

Duk da cewa hedikwatar tsaron ba ta tabbatar da yunƙurin juyin mulkin kai tsaye ba, amma kakakinta, Birgediya Janar Tukur Gusau, a ranar 4 ga watan Oktoba, ya ce ana binciken wasu sojoji 16 kan rashin ɗa’a da kuma saɓa ƙa’idojin aiki.

Sai dai sanarwar da Birgediya Janar Gusau ya fitar a ranar Asabar, ta ce raɗe-raɗin juyin mulki da ake ta yamaɗiɗi ba gaskiya ba ne.

“Rundunar sojin Najeriya na tabbatar da cewa rahoton na ƙarya ne baki ɗayansa,” a cewarsa.

“An dakatar da faretin Ranar ’Yanci ne saboda a bai wa shugaban ƙasa damar halartar wani taro a wajen Najeriya, da kuma mayar da hankali wajen yaƙi da ta’addanci da ’yan fashin daji.

“Binciken da ake yi wa jami’ai 16 kuma na yau da kullum ne da aka saba domin tabbatar da ɗa’a da ƙwarewar aiki. An kafa kwamatin bincike kuma za a sanar da sakamakon bincikensa.”

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rundunar Sojin Nijeriya tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi

Rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su tare da kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu wajen yin garkuwa da su a ƙauyen Euga da ke Ƙaramar hukumar Toro a jihar.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Ahmed Wakil ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da majiyar PUNCH Metro ta ruwaito ranar Laraba.

Majalisar Dattawa ta amince da Amupitan Shugaban INEC Za a kafa kamfanin ƙera kayan sola a Kano

A cewar sanarwar, aikin ceton waɗanda aka kuɓutar ya biyo bayan kiran gaggawa da wani ɗan unguwar ya yi ga hukumar ne.

Wakil ya ce, “A ranar 29 ga Satumba, 2025 da misalin ƙarfe 12:01 na tsakar dare rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta samu kiran gaggawa daga wani ɗan banga na unguwar, inda ya ba da rahoton harin da wasu da ba a san ko su wanene ba suka kai ga sace wasu maza uku daga ƙauyen Euga, a Ƙaramar hukumar Toro da suka haɗa da: Idi Umar da Idi Lawan da Musa Lawal.”

Ya ƙara da cewa, rundunar ’yan sandan ta yi gaggawar tattara jami’an rundunar ’yan sandan yankin Toro, na babban ofishin jami’an Toro da na ofishin Nabordo, tare da jami’an tsaro na yankin domin kai ɗauki ga lamarin.

“Rundunar haɗin gwiwa ta yi nasarar bin diddigin waɗanda ake zargin zuwa wajen ƙauyen tare da gudanar da aikin ƙwararru wanda ya kai ga ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Wakil ya ƙara da cewa, an kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a wannan lamarin.”

Waɗanda ake zargin sun haɗa da: Abubakar Usman da Adamu Alo da Abubakar Aliyu da Umar Habu da Abubakar Mamman Abubakar da kuma Shehu Samb.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Najeriya: Rahotanni Dangane Da Juyin Mulki Wa Shugaba Tinubu Ba Gaskiya Bane
  • DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki
  • An tsinci gawar wata mata a kusa da Jami’ar Tarayya a Yobe
  • Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU
  • NSCDC Ta Kama Wadanda Ake Zargi Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Kaduna
  • Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja
  • Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi
  • An kama ɓarayi da motocin da aka sace a Gombe
  • An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi