Leadership News Hausa:
2025-12-04@00:05:41 GMT

Yadda Ake Alkaki

Published: 19th, October 2025 GMT

Yadda Ake Alkaki

Abubuwan da ake bukata:

Garin Alkama (Flour), Kofi 3, Sukari Kofi 1, Man Gyada (Don Soya), Yis (Yeast) – Cokali 1,Ruwa dumi rabin kofi, Gishiri kadan, Madarar ruwa (ba dole ba)

Zuma ko syrup (domin jiko bayan an soya) idan ana so.

 

Yadda ake hadawa:

Da farko za a samu kwano a zuba ruwan dumi sannan a saka yis da dan sukari sai a barshi kamar minti 5 zuwa 10 don ya kumburo.

Sannan sai a samu wani kwano ko roba a zuba garin alkama da sukari da gishiri kadan sannan a zuba wannan hadin na yis da aka yi cikin garin, idan ana so za a iya zuba madara kadan saboda karin dandano.

Sannan sai a gauraya kullin sosai har sai ya yi laushi sannan kuma ba ya mannewa hannu, idan kuma ya yi tauri sai a dan kara ruwa kadan. Daga nan sai a rufe kullun abar shi a ajiye na kusan awa daya ya tashi domin yis din ya yi aiki kuma kullun ya narke.

 

Yadda za a nade shi:

Bayan ya tashi, sai a murza kullun a saman tebur, a yanka shi da wuka ko a yi masa siffofi kamar zobba, ko zare.

Sannan a zuba mai a abin suya a dora a wuta idan ya yi zafi sosai, sai a soya Alkakin har ya zama ruwan kasa-kasa (golden brown). A juya shi lokaci-lokaci domin ya yi daidai a kowane gefe.

 

Yadda za a jika shi:

Jiko da zuma ko Syrup:

Bayan an soya, sai a juye Alkaki din cikin zuma ko hadin syrup (sukari da ruwa da dan lemun tsami) don ya zama mai dandano da dan dandanon zaki.

Bayan ya huce kadan, sai a ci shi tare da shayi, nono, ko ruwa mai sanyi.

Alkaki na iya daukar kwanaki 2–3 ba tare da ya lalace ba idan an ajiye shi a busasshen wuri.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Girke-Girke Yadda Ake Gurasa Ta Semovita October 12, 2025 Girke-Girke Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice) October 4, 2025 Girke-Girke Yadda Ake Hada Sushi September 27, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta bayyana cewa Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma.

Mai magana da yawun Hamas, ya bayyana cewa duk da cewa kungiyar ta na girmama yarjejeniyar tsagaita wuta sosai, gwamnatin mamayar Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar, wanda ya tanadi dakatar da yaki da kuma cika alkawarinta.

Hazem Qassem, ya fayyace cewa ci gaba da neman gawarwakin fursunoni, duk da wahalhalun da suke fuskanta, yana nuna cikakken jajircewar kungiyar ga yarjejeniyar.

A wata hira da ya yi da Al Jazeera, ya kara da cewa Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar, wanda ke kawo cikas ga aiwatar da ita.

Kakakin ya jaddada cewa ci gaba da neman gawarwakin fursunonin Isra’ila, duk da mawuyacin hali, yana nuna cikakken jajircewar Hamas ga sharuddan yarjejeniyar.

Hazem Qassem ya kuma yi kira ga masu shiga tsakani da su matsa wa gwamnatin mamaye lamba don ta cika dukkan wajibai, gami da bude hanyar shiga tsakanin Rafah da kuma ƙaddamar da mataki na biyu na yarjejeniyar.  

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani December 1, 2025 Tawagar ECOWAS za ta je Guinea-Bissau, bayan juyin mulkin soji December 1, 2025 Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran December 1, 2025 Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi December 1, 2025 Maduro Ya Gargadi Amurka Game Da Hankoron Mamaye Rijiyoyin Mai Na Venezuela December 1, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa December 1, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran. December 1, 2025 Lebanon: Sakon Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma December 1, 2025 Ireland Ta Sauya Sunan Wurin Shakatawa Daga Na Shugaban  “Isra’ila” Zuwa Na Shahidiyar Falasdinu November 30, 2025  Gaza: Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI
  • An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela
  • Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10
  • Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza
  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma