Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta samu nasara a karo na biyu a gasar Firimiya ta Nijeriya (NPFL) bayan ta doke abokiyar hamayyarta Kano Pillars da ci 2–1 a wasan da suka buga a yau Lahadi a filin wasa na Sani Abacha, Kofar Mata, Kano.

Rabiu Ali, kyaftin ɗin Kano Pillars, ne ya fara jefa ƙwallo a ragar Barau FC a minti na 20 da fara wasa.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Ibrahim ya farke ƙwallon ga Barau FC a minti na 50, sai kuma Stanley da ya ƙara ta biyu wanda ya tabbatar wa Barau FC nasara a wasan.

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3 Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa

Ko da yake Barau FC ta samu nasara a wasan na yau, hakan bai hana ta komawa matsayi na 18 a teburin gasar Firimiya ba, yayin da Kano Pillars ta cigaba da zama a matsayi na 20.

Pillars na da maki 5 kacal daga wasanni 8 da ta buga a bana, yayin da Barau FC ke da maki 8 daga wasanni 8 — inda ta ci wasa biyu, aka doke ta sau biyu, sannan ta tashi canjaras a wasanni biyu. Wannan kuma ita ce shekara ta farko da Barau FC ke buga gasar Firimiya ta Nijeriya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya October 19, 2025 Wasanni Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya October 18, 2025 Wasanni Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba October 18, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kano Pillars

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

An tsara fara sauraron ƙarar a ranar 17 ga watan Nuwamba, 2025, a gaban Mai Shari’a Yusuf Ubale.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja October 17, 2025 Manyan Labarai Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura October 17, 2025 Manyan Labarai Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa October 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An saki Ɗan Uwa Rano bayan tsare shi kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano
  • Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan ƙara aure a Kano
  • Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan kara aure a Kano
  • An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitul-mali Da Wakilin Cinikayyar Amurka
  • Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya
  • Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba
  • Marzieh Jafari  Ta Dauki Lambar Yabo Ta Horar Da Mata Wasan Kwallon Kafa A Nahiyar Asia
  • Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn