Aminiya:
2025-10-19@20:04:51 GMT

An saki Ɗan Uwa Rano bayan tsare shi kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano

Published: 19th, October 2025 GMT

’Yan Sanda sun saki ɗan jaridar Kano, Ibrahim Ɗan Uwa Rano, bayan tsare shi da suka yi kan zargin ɓata sunan hadimin Gwamnan Jihar, Abdullahi Ibrahim Rogo.

An tsare Rano a Shiyyar ’Yan Sanda ta Ɗaya da ke Kano, bisa zargin ɓatanci.

Talauci ne babban maƙiyin ɗan Adam — Atiku ’Yan sanda sun tsare ɗan jarida kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano

Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam sun bayyana tsare shi a matsayin saɓa doka da kuma ƙoƙarin danne ’yancin ’yan jarida.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda cin zarafi Ɗan Uwa Rano Hadimin Gwamna

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ƙaddamar da shirin AGILE na tallafin karatun yara mata da tallafin gyaran makarantu, domin inganta ilimi a faɗin jihar.

A wajen bikin da aka gudanar a Otal ɗin Custodian, Gwamna Inuwa, wanda Mataimakinsa Dakta Manasseh Jatau, ya wakilta, ya ce gwamnati na da niyyar kawar da duk wani abin da ke hana yara mata zuwa makaranta.

’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe Ba mu ji dadin yi wa mahaifinmu afuwa tare da riƙaƙƙun masu laifi ba – Iyalan Herbert Macaulay

Ya ƙara da cewa: “Idan ka ilmantar da ’ya mace, ka ilmantar da al’umma gaba ɗaya; idan ka karfafe ta, ka karfafu zuri’a baki ɗaya.”

Gwamnan, ya gode wa Bankin Duniya, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, da Kwamitin AGILE saboda haɗin kansu wajen inganta ilimi a jihar.

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki tare da su domin ɗorewar shirin.

Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Gombe, Dokta Aishatu Umar Maigari, ta ce wannan shiri babban ci gaba ne wajen inganta makarantu da bunƙasa tsarin kula da su ta hannun SBMCs.

Ta buƙaci masu ruwa da tsaki su tabbatar da cewa an yi amfani da kuɗaɗen tallafin yadda ya kamata.

A nata ɓangaren, Kodinetar Shirin AGILE, Dokta Amina Haruna Abdul, ta ce dubban yara mata za su amfana da tallafin domin rage matsin tattalin arziƙi da ke hana su karatu.

Ta kuma yaba da jajircewar gwamnatin jihar, wajen tallafa wa ilimi, inda ta ce hakan zai ƙara wa yara mata ƙwarin gwiwa su ci gaba da neman ilimi a faɗin jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
  • Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna
  • ’Yan sanda sun tsare ɗan jarida kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano
  • JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi
  • Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan ƙara aure a Kano
  • Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan kara aure a Kano
  • An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano
  • Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata
  • Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn