‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe
Published: 18th, October 2025 GMT
Ya bayyana cewa a ‘yan watannin da suka gabata, rundunar ta kara kaimi wajen kai samame a wuraren da ake zargin yin laifuka a fadin jihar, a wani bangare na kokarinta na rage yawan shan miyagun kwayoyi da laifukan da suka shafi hakan, wadanda hukumomi ke cewa sau da dama su kan zama sanadin tashin hankali da aikata laifuka musamman tsakanin matasa.
“Lokacin da barayin suka hango tawagar sintiri na kusantowa, sai suka tsere, suka bar tarin miyagun kwayoyi da wasu haramtattun abubuwa a wurin,” in ji Abdullahi.
Mai magana da yawun rundunar ya lissafa abubuwan da aka kwato da suka hada da kwayoyin “Suck and Die,” Tramadol da Diazepam, inda ya ce an kwashe su gaba daya zuwa ofishin ‘yansanda domin ci gaba da bincike da daukar matakan da suka dace.
“Dukkan shaidun da aka kwato an tafi da su ofishin ‘yansanda, kuma bincike na ci gaba domin gano da kama wadanda suka tsere,” in ji shi.
Kwamishinan ‘yansanda, CP Bello Yahaya, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da samamen bisa gaggawa da kwarewa, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen yaki da laifuka da shan miyagun kwayoyi a Jihar Gombe.
“Rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa Gombe ta kasance jiha marar laifi da kuma marar miyagun kwayoyi,” in ji shi.
“Muna aikawa da gargadi mai karfi ga duk masu aikata laifuka da su daina duk wani nau’i na aikata laifi ko kuma su fuskanci fushin doka,” in ji CP Yahaya.
Ya kuma roki jama’a da su ci gaba da bin doka da oda tare da taimaka wa ‘yansanda da sahihan bayanai da za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.
“Muna kira ga al’umma da su rika sanar da ofishin ‘yansanda mafi kusa idan sun ga wani motsi ko aiki da suke shakka domin a dauki mataki cikin gaggawa,” in ji sanarwar.
A watan Afrilu, Rundunar ‘Yansandan Jihar Ogun ta gudanar da aikin tsaro na tsawon sa’o’i biyu a Sagamu Interchange bayan samun rahoton wani harin ‘yan fashi da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum a kan hanyar Lagos–Ibadan Expressway.
A cewar rundunar, kwamishinan ‘yan sanda Lanre Ogunlowo ne ya jagoranci duba wurin, inda aka gano haramtattun kasuwanin, ‘yan daba da kuma maboyar ‘yan ta’adda a cikin dazukan da ke kusa da wurin.
A lokacin aikin tsaron, an kama mutum uku da ake zargi, sannan kuma an kara tsaurara sintiri a yankin domin hana sake kai irin wannan hari a nan gaba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: miyagun kwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo
Rundunar ’yan sandan Jihar Oyo, ta tabbatar da kama wani mutum mai suna Lawal Faruƙ da ake zargin ya bankawa tsohuwar masoyiyarsa wuta bayan da dangantakar su ta yi tsami.
Majiyar PUNCH Metro ta samu labarin a ranar Alhamis cewa, lamarin ya faru ne a barikin sojoji da ke Ibadan babban birnin jihar.
Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi Ba mu ji dadin yi wa mahaifinmu afuwa tare da riƙaƙƙun masu laifi ba – Iyalan Herbert MacaulayWani ƙwararre a fagen yaƙi da ’yan tada ƙayar baya, Zagazola Makama wanda ya bayyana yadda lamarin ya faru a shafinsa na sada zumunta na X, ya bayyana cewa, wanda ake zargin ya yi iƙirarin cewa shi da budurwar sun yi rantsuwar cewa ba za su rabu ba.
Sai dai rahoton ya bayyana cewa, wanda ake zargin ya fusata ne bayan da dangantakar ta soyayya da ke tsakaninsu biyun ta lalace.
Lamarin da ya fusata saurayin wanda ake zargin ya zuba wa budurwar man fetur kafin ya banka mata wuta.
Bayan faruwar lamarin, jami’an soji da ke barikin sun ceto matar inda aka garzaya da ita zuwa asibiti kafin su kama wanda ake zargin.
Makama ya rubuta cewa, “Wacce aka kashen mai suna Omolola Hassan, an bada rahoton wanda ake zargin ya zuba mata man fetur sannan kuma ya ƙona ta, wanda aka ce ya fusata ne saboda taɓarɓarewar alaƙarsu.
“A cewar shaidu, jami’an soji da ke barikin sun yi gaggawar shiga tsakani tare da kashe wutar kafin a garzaya da budurwar zuwa asibitin Yawiri da ke Akobo don yi mata magani.
“Wanda ake zargin, wanda ya yi iƙirarin cewa dukkansu sun yi rantsuwar cewa ba za su rabu ba, a halin yanzu yana tsare.”