‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe
Published: 18th, October 2025 GMT
Ya bayyana cewa a ‘yan watannin da suka gabata, rundunar ta kara kaimi wajen kai samame a wuraren da ake zargin yin laifuka a fadin jihar, a wani bangare na kokarinta na rage yawan shan miyagun kwayoyi da laifukan da suka shafi hakan, wadanda hukumomi ke cewa sau da dama su kan zama sanadin tashin hankali da aikata laifuka musamman tsakanin matasa.
“Lokacin da barayin suka hango tawagar sintiri na kusantowa, sai suka tsere, suka bar tarin miyagun kwayoyi da wasu haramtattun abubuwa a wurin,” in ji Abdullahi.
Mai magana da yawun rundunar ya lissafa abubuwan da aka kwato da suka hada da kwayoyin “Suck and Die,” Tramadol da Diazepam, inda ya ce an kwashe su gaba daya zuwa ofishin ‘yansanda domin ci gaba da bincike da daukar matakan da suka dace.
“Dukkan shaidun da aka kwato an tafi da su ofishin ‘yansanda, kuma bincike na ci gaba domin gano da kama wadanda suka tsere,” in ji shi.
Kwamishinan ‘yansanda, CP Bello Yahaya, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da samamen bisa gaggawa da kwarewa, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da jajircewa wajen yaki da laifuka da shan miyagun kwayoyi a Jihar Gombe.
“Rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa Gombe ta kasance jiha marar laifi da kuma marar miyagun kwayoyi,” in ji shi.
“Muna aikawa da gargadi mai karfi ga duk masu aikata laifuka da su daina duk wani nau’i na aikata laifi ko kuma su fuskanci fushin doka,” in ji CP Yahaya.
Ya kuma roki jama’a da su ci gaba da bin doka da oda tare da taimaka wa ‘yansanda da sahihan bayanai da za su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.
“Muna kira ga al’umma da su rika sanar da ofishin ‘yansanda mafi kusa idan sun ga wani motsi ko aiki da suke shakka domin a dauki mataki cikin gaggawa,” in ji sanarwar.
A watan Afrilu, Rundunar ‘Yansandan Jihar Ogun ta gudanar da aikin tsaro na tsawon sa’o’i biyu a Sagamu Interchange bayan samun rahoton wani harin ‘yan fashi da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum a kan hanyar Lagos–Ibadan Expressway.
A cewar rundunar, kwamishinan ‘yan sanda Lanre Ogunlowo ne ya jagoranci duba wurin, inda aka gano haramtattun kasuwanin, ‘yan daba da kuma maboyar ‘yan ta’adda a cikin dazukan da ke kusa da wurin.
A lokacin aikin tsaron, an kama mutum uku da ake zargi, sannan kuma an kara tsaurara sintiri a yankin domin hana sake kai irin wannan hari a nan gaba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: miyagun kwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa masu ibada a Kogi
’Yan bindiga sun yi garkuwa da wani fasto da matarsa da mabiyansa a yayin da suke tsaka da ibada a coci da ke a Jihar Kogi.
Wani ganau da ke cikin cocin a lokacin da aka kai harin, Adegboyega Ogun, ya ce misalin ƙarfe 9.30 na safe ’yan bindigar suka kai harin suna bude wuta.
“Mutane sun qarshe ta ko’ina, har da faston, wanda aka fi sani da Baba Orlando da matarsa da wasu masu ibada duk an yi garkuwa da su. Gaskiya harin ya yi muni, dukkanmu tserewa muka yi daga cocin.”
Sace masu ibadar a ranar Lahadi a Cocin Cherubim and Seraphim ya auku ne bayan a kwanan nan Gwamna Usman Ododo, ya koka da cewa wasu manyan jagororin ’yan bindiga sun dawo jihar.
Kafin nan a ranar Asabar ’yan bindiga sun tare hanya, suka yi garkuwa da matafiya cikin motoci uku a kan hanyar Isanlu-MakutuIdofin da ke Ƙaramar Hukumar Yagba ta Gabas.
Wani mazaunin yankin, Enimola Daramola ya bayyana cewa, “mutum ɗaya ne kacal ya samu tserewa a motocin da aka tafi da su cikin daji.”
“Amma mun samu labari yau cewa sojoji da ’yan banga sun bi sawun ’yan bindigar inda suka yi musayar wuta suka ceto wasu daga cikin mutanen,”
A ranar Lahadi kuma aka samu rahoton cewa an kai wa wata motar haya hari.
“Matuƙin motar da fasinjojin sun tsallake rijiya da baya. Yanzu hanyar ta zama mai hatsari sosai,” in ji David Juwon, mazaunin yankin Isanlu.
Sabon harin Cocin Cherubim and Seraphim na zuwa ne makonni kaɗan bayan makarancinsa da ’yan bindiga suka sace mutane 38 a wani Cocin CAC da ke yankin Eruku na Karamar Hukumar Ekiti a Jihar Kwara.