Aminiya:
2025-10-20@10:45:15 GMT

Jami’an tsaro sun buɗe wa masu zanga-zangar Nnamdi Kanu wuta a Abuja

Published: 20th, October 2025 GMT

Masu zanga-zangar neman a sako jagoran ’yan awaren Biafra, Nnamdi Kanu sun watse bayan jami’an tsaro sun yi amfani da harsasai masu rai domin tarwatsa su.

A safiyar Litinin ɗin nan nan ne masu zanga-zangar suka fito kan titunan Abuja, duk da umarnin kotu da ta hana su zanga-zangar a kuma da a Fadar Shugaban Ƙasa.

Zanga-zangar ta samu jagorancin dan gwagwarmaya kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar African Action Congress (AAC), Omoyele Sowore, wanda shi ne mai jagorantar motsin #RevolutionNow.

Mutanen sun fara taruwa tun karfe 6:50 na safe a kusa da ofishin Ma’aikatar Harkokin Mata.

Shaidu sun ce jami’an tsawon haɗin gwiwar ’yan sanda, da sojoji da DSS da Sibil Difens (NSCDC) ne suka yi dirar mikiya wajen.

Jami’an tsaron sun fara tsaurara matakan tsaro tun ranar Lahadi a kusa da Fadar Shugaban Ƙasa da Majalisar Dokoki ta Ƙasa Kotun Daukaka Kara, da kuma Dandalin Eagle Square,  bayan masu zanga-zangar sun dage cewa sai sun isa har fadar shugaban ƙasa domin miƙa buƙatunsu kan ci gaba da tsare Nnamdi Kanu.

Shaidun sun ce rikicin ya fara ne bayan Sowore da wasu masu zanga-zanga suka fara rera wakokin goyon bayan #FreeNnamdiKanuNow yayin da suke ƙoƙarin wucewa kusa da Kotun Ɗaukaka Kara. Nan ne jami’an tsaro suka fara buɗe wuta.

Da farko masu zanga-zangar sun ɗauka cewa jami’an tsaron na harba barkonon tsohuwa ne, amma daga bisani aka tabbatar cewa harsasai na gaske ne ke tashi daga wurare daban-daban.

“Kada ku harba mana da barkonon tsohuwa! Ku mutunta doka! Muna da ’yanxin  yin zanga-zanga, mu ’yan Najeriya ne!” in ji Sowore cikin murya daya da sauran masu zanga-zangar.

Bayan wannan kalamai, sai aka fara harbe-harbe, wanda hakan ya sa jama’a suka fara gudu don tsira da rayukansu.

A lokacin da ake hada wannan rahoto, motocin sulke sojoji, ’yan sanda, da DSS suna nan a bakin aiki a muhimman hanyoyi kusa da tsakiyar birnin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro masu zanga zangar jami an tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe

Rundunar ’Yan sandan Jihar Gombe ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi da sauran laifuka, inda ta gudanar da samame a wata maɓoya da ake zargi da aikata ayyukan ta’addanci da safarar ƙwayoyi a cikin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, ta bayyana cewa jami’an da ke ƙarƙashin Gombe Division ne suka gudanar da samamen da misalin ƙarfe 9:00 na dare a ranar Alhamis 10 ga Oktoba, 2025.

Dantawaye ya zama sabon kwamishinan ’yan sandan Abuja Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo

A cewar sanarwar, jami’an sun kai samamen wata maɓoya da ke bayan jerin shagunan Ƙaramar hukumar Gombe, (Local Government Shopping Complex), inda ake zargin wasu fusatattun matasa ke gudanar da ayyuka irin na ta’ammali da miyagun ƙwayoyi.

“Da zarar matasan suka hangi isowar jami’anmu, suka tsere suka bar kayan ƙwayoyi da sauran haramtattun abubuwan da aka haramta,” in ji DSP Abdullahi.

Daga cikin abubuwan da aka ƙwato akwai nau’ukan miyagun ƙwayoyi kamar Suck and Die, Tramadol da allurarai na Diazepam.

An tura kayan shaida ɗin zuwa ofishin ’yan sanda domin ci gaba da bincike.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, CP Bello Yahaya ne ya tabbatar da ƙudirin rundunar na ci gaba da tabbatar da Gombe ta zauna lafiya an kuma tsarkake ta daga miyagun ƙwayoyi.

Ya kuma gargaɗi masu aikata laifuka da su daina irin waɗannan ayyuka ko kuma su fuskanci hukuncin doka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zanga-zanga: Jami’an tsaro sun kafa shingayen bincike a wajen Abuja
  • Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja
  • Nnamdi Kanu: Masu zanga-zanga sun yi watsi da gargaɗin ’yan sanda
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?
  • Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu
  • An tsinci gawar wata mata a kusa da Jami’ar Tarayya a Yobe
  • Zanga-Zangar Miliyoyi A Yemen Ta Jaddada Alkawari Ga Shahidai Da Ci Gaba Da Goyon Bayan Al’ummar Falasdinu
  • ’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe
  • Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi