Hamas ta yi Allah wadai da Isra’ila kan keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta
Published: 19th, October 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi Allah wadai da Isra’ila kan keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta, tare da yin Allah wadai da ci gaba da rufe mashigar Rafah a matsayin wani mataki na karan tsaye ga sulhun.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, Hamas ta yi Allah wadai da matakin da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya dauka na jinkirta bude mashigar Rafah tare da bayyana hakan a matsayin karya sharuddan tsagaita bude wuta da kuma kaucewa alkawurran da aka dauka ga masu shiga tsakani da masu bada garantin.
Kungiyar ta yi gargadin cewa rufewar yana kuma kawo cikas ga zuwan tawagogi na musamman domin zakulo gawarwakin da ke karkashin baraguzan gine gine da kuma gano wadanda suka mutu, ciki har da gawarwakin mutanen Isra’ila da aka yi garkuwa da su da za a mayar da su karkashin yarjejeniyar tsagaita bude wuta. Kungiyar masu fafutukar kare hakkin bil adama ta ce Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta sau 47 tun bayan aiwatar da ita a makon jiya, inda ta kashe Falasdinawa 38 tare da jikkata wasu 143 na daban
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An gudanar da zanga-zanga a sassa da dama na Amurka October 19, 2025 MDD : “Zai dauki lokaci” kafin a rage yunwa a Gaza October 19, 2025 ICC ta ki amincewa da daukaka karar Isra’ila October 19, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 159 October 19, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Hassan(a) 158 October 19, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Al-Hassan (a) 157 October 19, 2025 KissoshinRayuwa : Sirar Imam Al-Hassan(a) 156 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 155 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 154 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 153 October 19, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita bude wuta Allah wadai da
এছাড়াও পড়ুন:
Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 152
152-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littana wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Murtadha Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawa, na maulana jalaluddeen Rumi ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.
////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Hassan Al-Mujtaba(a) dan Fatimah diyar manzon All..(s) da muke kawo muku. Mun yi maganar yadda, aka kawo likitoci don jinyar Amirulmuminina(a). Inda shugaban likitocin Atthi dan Amru Assakuni ya bukaci a kawo masa jijiyar akuwa mai zafi sai aka kawo masa, ya Sanya ta cikin raunin da aka yi masa, bayan wani lokaci ya fitar da ita sai ya ga cewa fari-farin kwakwalwansa na makale a jikinta, sai ya tabbatar da cewa ba zai rayuba, saboda takobin ya kai cikin kwakwalwansa.
Daganan Imam (a) y afara wasiyoyinsa daban-daban da farko ga yayansa Imam Al-Hassan da Al-Hussain(a) sannan wasu ga iyalan gidansa da kuma yayansa. Wasun kuma ga duk wanda wasiyyar ta isheshi.
Sannan ya yi wa sauran musulmi ma iznin shiga wajensa inda ya bukacesu su tambaye shi kafin su rasa shi, inda suka yi masa tambayoyi, amma ba masu yawa ba don halin da yake ciki.
Daga karshe sai yayi wasiyya ga danga Imam Alhassan a matsayin khalifan al-ummar musulmi a bayansa. Sannan Alhusain (a) bayan Alhassan(a). Ya kafa shaidar hakan da sauran yayansa da manya-manyan malaman shi’a, sannan malaman shi’a basu da wani sabani dangane da hakan.
Daga ciki har da hadisin da Kulaini ya ruwaito, dangane da wasiyya , har zuwa inda yake cewa:
{Ya da na! Manzon Allah (s) ya umurce ni, da in yi wasiyya gareka, kuma in baka littafaina da makamaina, Kumar yadda manzon Allah (s) ya yi sanya ni wasiyyinsa, ya mika mani littafansa, da makamansa, kuma ya umurce ni da in umrceka kan cewa idan mutuwa ta zo maka ka mika su ga dan’uwanka Husain(a)}
Daga karshe ya ce masa shi ne waliyin jininsa, idan ya mutu. In yaga dama ya yi afwa in zai kashe kuma duka da duka.
Sannan muka ce wasu malaman sunna sun bayyana cewa Amirulmuminina (a) bai yi wasiyyah ba, kamar yadda suka ce manzon All..(s) ma bai yi wasiyya ba. Tare da dogara da wani hadisi wanda wanda shu’aib ya ruwaito, shu’ab wanda ya shahara da karyawa.
Don wasiyyar Imam Hassan da al-hussain (a), hadisan manzon All..(a) ne, wasu ma ayoyin Alkur’ani ne. su shuwagabannin Aljannae, ga Alhussain, yana cewa: Kai limami ne, dan Iimami ne, dan Uwar Imam sannan Baban limamai 9. Suna cikin ayar tsarkakiwa, suna cikin ayar mubahala, da sauransu.
Wadanda sun wadatar wajen tabbatar da cewa Imam Alhassan (a) wasiyyi ne daga cikin wasiyyan manzon All..(s).
Sannan yadda ko way a san Amirulmuminina (a) yake son hadin kan al-ummar musulmi, ba zai yu ya tafi ya bar al-ummar manzon Allah(s) ba tare da mai kula da su ba.
A lokacinda tafiyarsa ta karato y afara jin zafin ciwon da kuma mutuwa sai ya yawaita addu’o’io da zikirin Allah karshen abinda Kalmar da ta fito daga bakinsa itace {Saboda irin wannan to masu aiki su yi aiki} cikin suratul Saffaat aya ta 61.
Sannan ruhinsa ya fita, ya tafi aljanna firdauci, ya koma inda ya fito. Ya zo ya haskaka duniya da hasken shiriya, ya kuma huta da musibun duniya. Imam ya barma ilmin wanda al-ummar manzon All..(s) zata amfana da shi har duniya ta nade.
Ya bar mana tarin ayyuka da yayi tun haihuwarsa a dakin Kaaba har zuwa ranar da ya bar nan duniya, yana dan shekara 63 a duniya, bayan gwagwarmaya da mushrikai a makka, da kuma yakarsu a yakokin manzon All..(s) har iya yau da zama karshen wadanda suka kwace hakkinsa na kimani shekaru 25, da kuma shugabanci abin buka misali har duniya ta nade, da kuma yakar munafukai a jamal da siffin na Nahrawan.
Wannan shi ne Aliyu dan Abitalib Amirul muminina (a), taskar ilmin manzon All..(s) sannan Harunansa, kamar yadda annabi haruna yake ga Musa(a).
Imam Hassan (a) ne ya yi masa duk abinda akewa mamaci, kama daga wanka, hanuth da likkafani. Sannan bayan dare ya raba sai shi tare da wasu mutane daga iyalan gidansa suka Sanya shi a Najafur Ashraf, wanda a lokacin Daji ne. a bayan garin Kufa.
A lokacinda gari yaw aye sai Imam Al-Hassan (a) ya bukaci a kawo masa dan Mujam da aka kawo shi sai ya tambaye shi : Menen babanka ya umurceka dangane da ni? Sai Imam (a) ya amsa masa da cewa {Ya umurce ni da cewa kada in kashe sai wanda ya kashe shi. Kuma in cika maka cikinka, in gyara halinka, in yaru yayi kisasa ko ya yi afawa, idan kuma ya mutu in hadaka da shi}
Sai la’anennen yace: Duk da cewa babanka yana fadar gaskiya, amma yana hakan a cikin fushi da yarda.
Sai Imam Hassan (a) ya da kansa ya dauki takobi ya sare shi a kansa amma ya tare dukan da hannayensa. Sai ya kashe kawai. Bai yi muthla da shi ba.
A cikin wasu littafn tarihi, an bayyana cewa wai Imam Hassan yayi Muthla da shi duk tare da nanatawa da mahaifinsa yayi na kada ya yi hakan.
Ko kuma wasu sun bayyana cewa wasu daga cikin yayan Iman Ali (a) suka yi muthla da shi. Sun kuma kawo hadisai da ruwayoyi da suke nuna hakan.
Sai dai wannan zatonsu ne ga iyalan gidan manzon All…(a) sai. Amma gidan tsarki da annabta sun wuce nan, ba wanda zai wuce su a riko da shari’ar Allah ta’ala.
Sannan sabanin da ce cikin hadisan da suka ruwaito na haka ya faru ya tabbatar da cewa zancen karyace ce.
Daga cikin wadanda suka kawo wadannan ruwayoyi na karya suke kuma ganin gaskiya ne haka ya faru, akwai Dr Taha Hussain a cikin littafinsa ‘Aliyu wa banuhu’. Sai dai gaskiyar al-amarin ba haka bane basu yi muthla da shi ba.
Bayan jana’iza da kuma kisasi kan Abdurrahman dan Muljamul Muradi, sai batun bai’a wa Imam Al-Hassan (a). wanda ya kasance a cikin wani hali na rashin tsaro a cikin daular Musulunci.
Imam Hassan (a) ya gaji rundunar mahaifinsa wacce taki fida don yakar Mu’awiya, sannan mu’awiya na na ci gaba da mamayar ragowar yankunan da suke karkashin ikon Amirul muminina Aliyu dan Abutalib (a), wanda Imam Alhassan ya gada.
Sannan shahadar Imam Ali (a) ya karawa Mu’awiya dan Abusufyan karfin giwa na cewa zai iya samun nasara a kan Imam Hassan ya kuma mallaki dukkan daular musulunci, sannan wannan ya sharewa babu umayya hanyar maida khalifanci gadon gidansu. Da kuma shimfida zalunci da kissan al-ummar musulmi da dandana masu azaban da basu tsamman zai faru ba, kafin haka.
Ya zuwa shahadar Imam Ali(a) mu’awiya ya kwace Makka da Madina da yemen da Masar bayan kissan Muhammad dan Abubakar da kuma Malikul Ashatar. Kasar Iraki kadai ta rage a hannunsa zuwa lokacin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 151 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 150 October 19, 2025 Wata Kotun A Murka Ta Haramtawa HKI Kafa Na’urorin Leken Asiri A Wayoyi Masu WattsApp October 19, 2025 Sojojin Najeriya: Rahotanni Dangane Da Juyin Mulki Wa Shugaba Tinubu Ba Gaskiya Bane October 19, 2025 Hamas Ta Gabatar Da Sunayen Kwararrun Da Zasu Gudanar Da Harkokin Gaza October 19, 2025 Doha: Pakistan da Afghanistan sun amince da tsagaita bude wuta a tsakaninsu October 19, 2025 Isra’ila ta ce mashigar Rafah za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai abin da hali ya yi October 19, 2025 Araqchi: Kuduri Mai Lamba 2231 Ya Zo Karshe October 18, 2025 Kasashen Iran, Rasha, Da China Sun Jaddada Rashin Halaccin Dawo Da Tsohon Takunkumi Kan Iran October 18, 2025 Masani Kan Harkokin Tsaro Ya Ce: Makami Mai Linzamin Iran Kirar Ghadir Ya Aike Da Sako Ga Isra’ila October 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci