An tsinci gawar wata mata a kusa da Jami’ar Tarayya a Yobe
Published: 18th, October 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta gano gawar wata mata mai suna Falmata Abubakar, mai kimanin shekaru 45, wadda aka kashe a kusa da Jami’ar Tarayya Gashuwa (FUGA), da ke Ƙaramar Hukumar Bade.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7 na safe a ranar 17 ga watan Oktoba, 2025, bayan wani mazaunin unguwar Sabon Daula mai suna Yusuf Sarkin Baka, ya kai rahotn ganin gawar.
’Yan sanda sun isa wajen, inda suka tabbatar cewa mamaciyar ita ce Falmata Abubakar, mazauniyar Abasha, unguwar Sarkin Hausawa.
An same ta sanye da baƙin hijabi, kwance babu rai.
An kai gawar Asibitin Ƙwararru na Gashuwa, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarta.
Bayan kammala bincike, an miƙa iyalanta gawarta domin yi mata jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
Rahotanni sun nuna cewa an jefar da gawar marigayiyar ne, kimanin kilomita biyu da gidanta.
Kwamishinan ’yan sandan Jihar Yobe, CP Emmanuel Ado, ya tabbatar da cewa rundunar ta fara bincike domin gano waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki.
Ya kuma roƙi jama’a su kwantar da hankalinsu, tare da bai wa ’yan sanda haɗin wajen bincike.
Rundunar ta jaddada ƙudirinta na kare rayuka, dukiyoyi da tabbatar da zaman lafiya a faɗin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Gawa Wata mata
এছাড়াও পড়ুন:
Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU
Ya ce “Daga wancan lokacin zuwa yanzu, mun rasa Farsesoshi 309,wasu sun je Jami’oi masu zaman kansu a Nijeriya, sauran wasu sun je London, Saudi Arebiya, Kameroon da kuma wasu kasashe.Kwarrunmu wadanda babban jari ne suna barin aiki saboda sharuddan aikinsu babu wani abin jin dadin da zai sasu ci gaba da kasancewa wuraren aikinsu na koyarwa kamar yadda ya ce,”.
Sabo ya bayyana cewa kungiyar za ta fara yajin aikin mako biyu daga ranar Litinin, idan har gwamnatin tarayya ta ci gaba watsi da maganar bukatunta da kuma inganta masu sharuddan aiki.
“Mun yi shiru har abin ya wuce misali.Hakkin mune nu ceto jami’oin gwamnati. Idan har gwamnati ta ci gaba da yin biris da mu, ba zamu ci gaba da sa ido ba yayin da lamarin ilimi yana kara durkushewa.
“Da muka bada wa’adin mako biyu, gwamnati ta farakiran waya ne, daganan suka fara kiran kungiyoyi kamar na makarantun fasaha, da Kwalejojin ilimi domin su kara dagula lamarin cewar akwai wani kokarin da ake na kawo matsala samar da matsaloli kan kasafin kudin ilimi domin dakushe irin gwagwarmayar samun bukatunsu da suke kamar yadda ya yi zargi,”.
Tun farko ne Shugaban kungiyar na ASUU-UDUS, Farfesa. Muhammad Almustapha, ya ce taron an kira shi ne domin a sanar da ‘yan Nijeriya dangane da irin koma bayan da ake samu a ilmin Jami’oi, da kuma gazawar gwamnati ta cika ma kungiyar alkawuran data yi.
“Shekarun da suka gabata, kungiyar ASUU ta saba da tafiye- tafiye yajin aiki, saboda yana da matukar wuya gwamnati ta cika alkawuran da ta yi. Abin ya zama alkawari bias wani alkawarin da, ba za’a cika ba duk kuma wani tunanin da kungiyar take abin ya zama kanzon Kurege kama yadda ya jaddada”.
Kungiyar ta yi kira da gwamnati ta dauki mataki na gaggawa domin ta kawo karshe karshen yadda kwararru suke barin aikin koyarwa, domin a shawo kan kara lalacewar ilimin jami’a a Nijeriya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA