A wani jawabin da aka yada ta kafar sadarwar zamani ta shafin Facebook jiya, ma’aikatar ta kara da cewa tun lokacin da shi Gwamnan ya dare kan Kujerar mulkin Jihar, mulkin gwamna Inuwa ya kafa dokar ta baci kan lamarin daya shafi ilimi, inda ya bullo da tsare tsare da zuba jari da zummar bunkasa bangaren ilimiin.

 

Wadanda za su amfana da karin tallafin kudin karatun sun hada dalibai masu karatun da suka hada da PhD, MSc, PGD, BSc, HND, NCE, ND, da kuma Satifiket.

 

Da yake na shi jawabin wajen sa albarkacin baki kan ci gaban da aka samu, Shugaban kungiyar dalibai ‘yan asalin Jihar da suke Jami’ar Jihar Gombe, Abubakar Muhammad Yamanga, ya bayyanawa LEADERSHIP cewa alawus din da dalibai suke amsa yanzu Naira 7,500, ko dayake dais au da yawa su kan amshi Naira 7,000 bayan wasu cire- ciren da aka yi.

 

“Wannan ya nuna da yake an riga an bayyana karin, da aka yi, ana kuma sa ran dalibai za su rika amsar fiye da Naira 14, 000. Tuni dai aka riga aka biya Naira 21,000 kowane inda aka biya wasu kudaden da, ba a biya ba can baya,” in ji shi

 

Kamar dai yadda ma’aikatar ilimi mai zurfi ta bayyana, gwamnan ya amince da karin da aka yiwa mutane masu bukata ta musamman, jim kadan bayan da aka kirkiro hukumar kulawa da lamurran masu bukata ta musamman ta Jihar.

 

Hukumar bada tallafin karatu ta Jihar Gombe ta bada sanarwar lamarin tantancewa da za ayi domin a samu gano dukkan daliban da suka cancanta su amfana, za a fara cancancewar nan bada dadewa ba da kuma ranakun da za ayi haka, da kuma duk yadda za ayi ita tantancewar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ilimi Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma October 18, 2025 Ilimi Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU October 18, 2025 Ilimi Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba October 13, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Kwara Zata Haɗin Kai Da Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Horas Da Matasa Fasahar AI

Ma’aikatar raya matasa ta jihar Kwara tare da hadin gwiwar Masu Ruwa da Tsaki don horar da matasa kan amfani da fasahar AI don ganin sun kasance masu amfani da dogaro da kai, da kuma samun fasaha.

 

Da yake jawabi a lokacin da tawagar ta ziyarci ma’aikatar a Ilorin, kwamishinan ci gaban matasa na jihar, Ndanusa Shehu, ya bayyana matakin a matsayin wanda ya dace kuma ya kawo sauyi.

 

A cewarsa Artificial Intelligence wata hanya ce ta tsara makomar aiki a duniya tare da jaddada mahimmancin ganin matasa sun iya amfani da irin wannan kirkirarriyar fasaha.

 

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta ci gaba da nuna kyakykyawan manufa na karfafa matasa, tun daga samar da damammaki a fannin tattalin arzikin dijital zuwa saka hannun jari a fannonin fasaha da kasuwanci.

 

A nasa bangaren masu, Daraktan Sadarwa, Sanni Alausa-Issa ya ce shirin ya himmatu wajen inganta shugabanci na gari, hada kan jama’a, da ci gaban matasa ta hanyar ilimi na zamani.

 

ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
  • JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i
  • Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi
  • Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata
  • Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 6 Don Bunkasa Noma, Ilimi Da Kasuwanci
  • ’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafin Kayayyakin Sana’o’i A Karamar Hukumar Gagarawa
  • Jihar Kwara Zata Haɗin Kai Da Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Horas Da Matasa Fasahar AI
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cire Darasin Lissafi Zai Taimakawa Dalibai Shiga Jami’a