Aminiya:
2025-10-18@22:25:42 GMT

An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano

Published: 18th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta kama wasu ’yan sandan bogi guda biyar, da ke damfarar jama’a wajen karɓar kuɗi a Kano, Katsina da kuma Kaduna.

Waɗanda ake zargin sun haɗa Aliyu Abbas mai shekaru 35, Sani Iliyasu mai shekaru 47, Ashiru Sule mai shekaru 41, Abubakar Yahaya mai shekaru 45 da kuma Adamu Kalilu mai shekaru 45.

Matasa sun yi zanga-zanga kan yunwa a Adamawa Sojoji sun tallafa wa mutanen Yobe da N23m bayan harin kuskure

Sashe na Musamman na Rundunar SIS ne, ya kama su a ranar 16 ga watan Oktoba, 2025, bayan samin wasu  bayanan sirri.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, yatabbatar da kama su.

Yayin bincike, an samu katin bogi ’yan sanda, ankwa, latattun kuɗi da motarsu ƙirar Peugeot 406 mai launin shuɗi mai lambar NSR-188-BD.

SP Kiyawa, ya bayyana cewa bincike ya gano cewa ƙungiyar tana amfani da katunan bogi wajen yin damfara, tsoratar da direbobi, da karɓar kuɗi a hannun jama’a a sassan Arewa maso Yamma.

“Waɗanda ake zargin sun amsa cewa ’yan sandan bogi ne kuma suna aikata laifuka daban-daban na damfara.

“Za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike,” in ji Kiyawa.

Kwamishinan ’yan sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya yaba wa jami’an rundunar saboda ƙwarewarsu wajen cafke waɗanda ake zargin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Yan sandan bogi bayanan sirri mai shekaru

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

 

Ya ce kamar ko da yaushe, kasar Sin za ta ci gaba da goyon bayan muhimmiyar rawar da FAO ke takawa a bangaren aikin gona da samar da abinci a duniya.

 

An kafa hukumar FAO ne a ranar 16 ga watan Oktoban shekara ta 1945, kuma Sin na daya daga cikin kasashe mambobi da suka kafa ta. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar? October 16, 2025 Daga Birnin Sin Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin October 16, 2025 Daga Birnin Sin Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya October 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn
  • Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo
  • Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
  • An kama ɓarayi da motocin da aka sace a Gombe
  • An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi
  • Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta, Isra’ila ta kashe Falasdinawa 3 a Gaza
  • ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano
  • An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.