An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano
Published: 18th, October 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta kama wasu ’yan sandan bogi guda biyar, da ke damfarar jama’a wajen karɓar kuɗi a Kano, Katsina da kuma Kaduna.
Waɗanda ake zargin sun haɗa Aliyu Abbas mai shekaru 35, Sani Iliyasu mai shekaru 47, Ashiru Sule mai shekaru 41, Abubakar Yahaya mai shekaru 45 da kuma Adamu Kalilu mai shekaru 45.
Sashe na Musamman na Rundunar SIS ne, ya kama su a ranar 16 ga watan Oktoba, 2025, bayan samin wasu bayanan sirri.
Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, yatabbatar da kama su.
Yayin bincike, an samu katin bogi ’yan sanda, ankwa, latattun kuɗi da motarsu ƙirar Peugeot 406 mai launin shuɗi mai lambar NSR-188-BD.
SP Kiyawa, ya bayyana cewa bincike ya gano cewa ƙungiyar tana amfani da katunan bogi wajen yin damfara, tsoratar da direbobi, da karɓar kuɗi a hannun jama’a a sassan Arewa maso Yamma.
“Waɗanda ake zargin sun amsa cewa ’yan sandan bogi ne kuma suna aikata laifuka daban-daban na damfara.
“Za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike,” in ji Kiyawa.
Kwamishinan ’yan sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya yaba wa jami’an rundunar saboda ƙwarewarsu wajen cafke waɗanda ake zargin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Yan sandan bogi bayanan sirri mai shekaru
এছাড়াও পড়ুন:
An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
Fargaba ta lulluɓe al’ummar Ungwan Nungu da ke gundumar Bokana a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna, bayan wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da mazauna yankin 11 a ranar Asabar yayin da suke dawowa daga gonakinsu.
Mazauna yankin sun ce an tare mutanen ne a wata hanyar daji da ke kusa da unguwar da yamma, inda aka tafi da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.
Lamarin ya tayar da hankula a ƙauyukan da ke kewaye, inda iyalai da dama suka kwana cikin fargaba.
Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu cewa wasu daga cikin waɗanda aka sace matasa ne da suka tafi gona domin yin roron wake lokacin da aka afka musu.
NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a JigawaYa ce: “An fara kai hari ne ga mutane 15, wasu sun tsere, wasu kuma aka sake su ba tare da sharaɗi ba. Amma har yanzu mutum 11 suna hannun ’yan bindiga, kuma sun buƙaci a biya su kuɗin fansa na naira miliyan biyar,” in ji shi.
Da yake tabbatar da afkuwar lamarin cikin wata sanarwa a ranar Talata, ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazavar Jama’a/Sanga, Hon. Daniel Amos, ya bayyana satar mutanen a matsayin mugunta da rashin tausayi, tare da yin Allah-wadai da kai hari kan talakawa masu aikin halaliya.
“Muna buƙatar kara tsaurara tsaro, yin amfani da dabarun bayanan sirri, da ɗaukar matakan gaggawa da haɗin gwiwa domin kwantar da hankalin jama’a da kuma ceto waxa0nda aka sace,” in ji shi.