Gwamnatin Jigawa Ta Jinjinawa UNICEF Da EU Bisa Gudunmawarsu A Fannin Ilimi
Published: 18th, October 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta yaba wa Hukumar Kula da Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) da Tarayyar Turai (EU) bisa gudunmawar su wajen inganta harkar ilimi a fadin jihar.
Shugaban Hukumar Ilimin Firamare (SUBEB) na jihar, Farfesa Haruna Musa, ne ya bayyana hakan a lokacin bude taron bitar kwana uku na karkashin Shirin Ayyukan Sashen Ilimi na a Jihar, wato Local Education Sector Operations Plan (LESOP) da aka gudanar a Dutse.
Ya bayyana cewa UNICEF da Tarayyar Turai na tallafa wa gwamnatin jihar ta hanyar Shirin Inganta Ilimi da Karfafa Matasa da Shirin Ayyukan Sashen Ilimi na jihar Jigawa inda ake sake dubawa da tsara sabbin tsare-tsaren aiki da za su zama jagora wajen inganta harkar ilimi a jihar.
A cewarsa, wannan shiri zai mai da hankali kan magance matsalolin da suka addabi tsarin ilimi, musamman matsalar karancin sakamako mai kyau a fannin koyo da kuma yawaitar yaran da ba sa zuwa makaranta.
A nasa jawabin, Manajan Ilimi na ofishin UNICEF na Kano, Mista Michael Banda, ya sake jaddada kudirin UNICEF din na ci gaba da hada kai da gwamnatin Jigawa wajen farfado da fannin ilimin firamare. Ya ce bitar LESOP muhimmin mataki ne wajen karfafa tsarin shiryawa da aiwatar da manufofin ilimi a jihar.
Mista Banda ya ce sake duba LESOP na nuna cewa gwamnatin jihar tana da niyyar bin sahihin tsarin yanke shawara bisa hujja, gaskiya da kuma hada al’umma, wadanda su ne muhimman ginshikan sauya tsarin ilimi a matakin ƙananan hukumomi.
Sai dai ya nuna damuwa cewa duk da ci gaban da aka samu, har yanzu yara da dama a Jigawa na fuskantar matsaloli wajen samun ingantaccen ilimi saboda talauci, aikatau, aurar da kananan yara ko kuma nisan makaranta daga gida. Ya ce tsarin LESOP zai ba da damar gano wadannan matsaloli a kowane yanki da kuma tsara mafita da suka dace da al’ummar yankin.
Ya kuma bayyana cewa rashin isassun kudade na daga cikin manyan kalubalen da ke hana cimma burin ilimi, tare da bukatar tabbatar da gaskiya wajen amfani da kudaden da aka ware. Ya bukaci gwamnati da ta nemi hanyoyin kirkire-kirkire wajen samar da kudade da kuma tabbatar da cewa kudaden da aka ware don ilimi sun isa makarantu akan lokaci.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa UNICEF
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran
Rahotanni sun bayyana cewa ministan harkokin wajen kasar Turkiya ya iso birnin Tehran a jiya lahadi kuma ya samu kyakkyawar tarba daga takwaransa na kasar iran Abbas Araqchi.
Ziyarar tasa ana saran za ta kara fadada dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, ganin cewa dukkan kasashen biyu suna taka rawa a batutun da suka shafi yanki dama duniya baki daya.
Bugu da kari bayan ganawarsa da Araqchi da musayar ra’ayoyi kan batutuwa daban daban, zai gana da sauran manyan jami’an gwammnatin kasar, da ake saran za su tattauna kan alakar dake tsakaninsu da kuma irin ci gaban da aka samu a yankin da dai sauran batutuwa na kasa da kasa.
Ana sa bangaren shugaban kasar iran Masud pezeshkiyan a lokacin ganawarsa da Hakan fidan ministan harkokin wajen kasar turkiya ya jaddada game da muhimmancin hadin kan kasashen musulmi cikin gaggawa, yace ya kamata kasashen musulmi su rike duba yanayi da yan uwansu suke ciki, kuma a nisanci tsaurara alamura, adaidai lokacin da suke fuskantar matsin lamba daga kasashen waje.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkian: Makiya na neman kawo cikas ga ci gaban kasashen Musulmi December 1, 2025 Shugaban Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar December 1, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa December 1, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran. December 1, 2025 Lebanon: Sakon Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma December 1, 2025 Ireland Ta Sauya Sunan Wurin Shakatawa Daga Na Shugaban “Isra’ila” Zuwa Na Shahidiyar Falasdinu November 30, 2025 Gaza: Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki November 30, 2025 Washington Post: Shirin Trump Na Kai Sojojin Gaza Yana Fuskantar Matsala November 30, 2025 MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari November 30, 2025 An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Turkiya November 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci