Aminiya:
2025-10-19@16:33:21 GMT

’Yan sanda sun tsare ɗan jarida kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano

Published: 19th, October 2025 GMT

’Yan sanda sun kama ɗan jarida Ibrahim Ishaq Dan’uwa Rano, kan zargin ɓata sunan Babban Hadimin Gwamnan Kano kan Al’amuran Fadar Gwamnati, Abdullahi Ibrahim Rogo.

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an ’yan sanda daga Hedikwata ta Ɗaya ne suka kama Dan’uwa Rano a ranar Asabar yayin da yake aiki a ofishinsa da ke Kano.

Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan ƙara aure a Kano Gwamnati ta ɗauki matakin rage shan gishiri a Nijeriya

Shaidu sun ce an kama shi ba tare da gabatar da takardar izinin kama shi ba.

Ana tsare da ɗan jaridar ne bisa zargin ɓata sunan hadimin cikin wani shirin barkwanci mai suna ‘Imalu’ da yake wallafawa a shafinsa na YouTube mai suna ‘Dan’uwa TV‘.

An ce ɗan jaridar ya yi shaguɓe a cikin shirin inda ya yi magana a kan hadimin tare da zarginsa da karɓar cin hanci don bai wa mutane damar ganawa da gwamnan.

Ko da yake bai ambaci suna ba a cikin shirin ba, Rogo, ya kai wa ’yan sanda ƙara, inda ya ce ana amfani da shirin wajen ɓata masa suna.

Dan’uwa Rano, ya tabbatar cewa ana yi masa tambayoyi kan shirin da kuma zargin gudanar da tasha a in5tanet ba tare da lasisin Hukumar NBC ba.

“‘Yan sanda sun ce ba mu da lasisi daga NBC, kuma kamfaninmu bai yi rijista ba,” in ji shi.

Kakakin ’yan sanda na Shiyya ta Ɗaya, CSP Bashir Muhammad, ya tabbatar da kama ɗan jaridar, inda ya ce an kama shi ne bayan ƙorafin ɓata suna da aka shigar a kansa.

Ya ce: “Babban Sufeton ’Yan Sanda na Shiyya ta Ɗaya, AIG Ahmed Garba, ya bayar da umarnin a gayyaci ɗan jaridar don yi. bincike. Bayan bincike, idan an same shi da laifi, za a gurfanar da shi a kotu.”

AIG Garba, ya kuma shawarci ’yan jarida da su tabbatar da adalci a cikin rahotanninsu tare da tuntuɓar ofishin hulɗa da jama’a na ’yan sanda kafin wallafa labarai.

Ya kuma nemi su bari ana gudanar da bincike ba tare da yin katsalandan ba.

’Yan sanda sun tabbatar da cewa za su yi bincike cikin gaskiya da adalci, kuma za a sanar da jama’a sakamakon abin da suka samu.

Idan ba a manta ba, Aminiya ta ruwaito EFCC da ICPC na binciken Abdullahi Rogo bisa zargin almundahanar kuɗi Naira biliyan 6.5.

Ana zargin ya karkatar da kuɗaɗen gwamnati ta amfani da wasu abokan hulɗarsa tsakanin watan Nuwamban 2023 da Fabrairun 2025.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Jarida Ɗan Jarida Ɗan Uwa Rano Yan sanda sun ɗan jaridar

এছাড়াও পড়ুন:

Matasa sun yi zanga-zanga kan yunwa a Adamawa

Wasu gungun matasa sun gudanar da zanga-zangar lumana a garin Yola da ke Jihar Adamawa, don jan hankalin gwamnati kan ƙaruwar talauci da yunwa.

Masu zanga-zangar sun bin manyan tituna, inda suka yi kira ga  Gwamnatin Tarayya da ta jihar da su ɗauki matakan rage wahala, rashin aikin yi da matsalar tsaro da ta addabi ƙasa.

Wasu jiga-jigan ADC za su dawo jam’iyyarmu — Shugaban APC HOTUNA: Al’ummar Jihar Neja sun yi addu’o’in neman zaman lafiya

Shugaban Ƙungiyar MOTION na Jihar Adamawa, Mista Musa Andrew, ya ce zanga-zangar ta zama dole ne saboda halin matsin tattalin arziƙi da ke ƙara taɓarɓarewa.

“Mun fito ne don mu yi magana kan rashin adalci da wahala, ga yunwa na ƙaruwa,” in ji shi.

“Yawancin ’yan Najeriya suna kwanciya ba tare da cin abinci ba, yara kuma suna zuwa makaranta ba tare da sun ci abinci ba. Rayuwa ta yi tsada sosai.”

Ya kuma bayyana damuwa kan matsalar tsaro da ke ƙara ta’azzara musamman a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma.

“Mun gaji da rashin tsaro a Arewa maso Gabas, Arewa maso Yamma da sauran sassan ƙasar nan. Yawancin matasanmu, sojoji da ’yan sanda suna rasa rayukansu a kullum,” in ji shi.

Andrew, ya yi kira ga gwamnati ta ɗauki matakai don tabbatar da daidaiton rabon albarkatun ƙasa tare da gyara tsarin fansho wanda ya ce yana cike da cin hanci.

“’Yan sanda suna yin ritaya suna komawa gida da kashi 40 cikin 100 na fanshonsu, sauran kuma ana wawurewa. Ba za mu lamunci wannan zalunci ba,” a cewarsa.

Ya kuma nemi a bai wa matasa dama su shiga harkae shugabanci.

“Yawancin shugabanninmu sun fara shugabanci tun suna da shekaru 20, amma yanzu sun ƙi bai wa matasa dama. Shugabanci ba gado ba ne,” in ji shi.

Ɗaya daga cikin masu zanga-zangar, Hajiya Blessing Musa, ta koka kan tsadar rayuwa, inda ta ce a yanzu magidanta da dama ba sa iya sayan kayan abinci.

“Yunwa tana kashe mu. Farashin kayan abinci ya yi tsada sosai, kuma ba mu da kuɗin saye,” in ji ta.

“Wani mutum ya roƙe ni na sayi shinkafa kan Naira 1,400 amma ba zan iya saya ba. Sama da kashi 70 cikin 100 na ’yan Najeriya suna rayuwa cikin talauci.

“Ba za mu iya tura ’ya’yanmu makarantu masu kyau ba, saboda na gwamnati ba sa aiki yadda ya kamata.”

Ta roƙi gwamnati ta ɗauki matakai don rage talauci, sauƙaƙa farashin abinci da kuma inganta makarantun gwamnati.

Mista Dennis Babangida, wani jagoran matasa, ya bayyana cewa yunwa ta yi ƙamari a Arewa kuma abun damuwa ce.

Ya nemi gwamnati ta tallafa wa manoma da kuma ƙirƙiro ayyukan yi domin rage talauci.

“Farashin taki ya yi tsada sosai, manoma ba sa iya saya. Idan gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma da kuma samar da ayyukan yi, hakan zai rage talauci da yunwa,” in ji Babangida.

Ya kuma gargaɗi gwamnati cewa idan ta ci gaba da yin shiru, matsalar yunwa na iya haddasa rikice-rikice a tsakanin jama’a.

“Jama’a suna jin yunwa kuma suna jin haushi. Gwamnati ta gaggauta ɗaukar mataki kafin lamarin ya fi haka muni,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi
  • Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan ƙara aure a Kano
  • Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan kara aure a Kano
  • An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano
  • Matasa sun yi zanga-zanga kan yunwa a Adamawa
  • Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano
  • Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata
  • Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn
  • An kama ɓarayi da motocin da aka sace a Gombe