Ya kara da cewa, Allah ya albarkaci Jihar Taraba da dimbin dabbobi, wanda kuma gwamnatin jihar za ta yi dukkan mai yiwuwa, wajen samar da kayan aiki tare da kara bunkasa fannin kiwo na jihar.

 

Kazalika, ya sanar da cewa; gwamnatin za kuma ta tabbatar da ta kara bunkasa kasuwancin fannin, musamman domin wadanda suke a fannin su kara samun kudaden shiga tare da kuma kara samar wa da gwamnatin kudaden shiga.

 

Nicholas, ya sanar da hakan ne, ta bakin wakilinsa Daraktan Kula da Harkokin Dabbobi da ke Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci na jihar, Daudu A. Mbaamo

 

Kwamishinan ya ci gaba da cewa, har yanzu fannin aikin noma, da shi jihar ta dogara a kai, musamman duba da cewa; fannin na bayar da gudumawa wajen kara samar da wadataccen abinci a jihar da kuma kara samar da ayyukan yi.

 

Haka zalika, ya koka da cewa; duk a irin wadannan dimbin albarkatun noma da kuma yawan dabbobin da Allah ya wadaci jihar da su, amma har yanzu jihar na ci gaba da fuskantar kalubalen karancin kasuwannin sayar da dabbobin.

 

Kwamishinan ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta himmatu, wajen kara habaka fannin kiwon jihar, wanda tuni ta tuntubi ‘yan kwangilar da za su yi aikin gyaran mayankar tare kuma da samar da kayan aiki na bunkasa kiwon dabbobi a jihar.

 

“Fannin kiwon dabbobi, na daya daga cikin fannonin da ke habaka tattalin arzikin Jihar Taraba da samar da wadataccen abinci da samar da ayyukan yi da kuma kara samar da kudaden shiga, “ a cewar Kwamishinan.

 

“Hakan ne ya sanya gwamnatin jihar, za ta samar da kayan aiki a fannin kiwon jihar, musamman domin cin gajiyar da ake da ita, daga fannin wanda kuma hakan zai amfanar da al’ummar jihar, in ji Nicholas.

 

A jawabinsa tun da farko, jami’in aikin tallafa wa kiwon dabbobi na L-PRES Hananiah Albert, ya jaddda kudurin aikin wajen ganin an cimma burin da aka sanya a gaba.

 

“Za mu tabbatar da mun bi dukkannin ka’idojin da suka dace, wajen wanzar da wannan aiki, domin cimma nasarar da aka sanya a gaba, “in ji Albert.

 

Ya kara da cewa, manufar aikin ita ce; domin mayar da hankali wajen habaka fannin hada-hadar kasuwancin kiwon na dabbobi da kuma kara bunkasa tattalin arzikin fannin tare da tabbatar da kula da lafiyar dabbobi a fadin jihar.

 

A cewarsa, a yanzu haka; akwai sama da kasuwannin sayar da dabbobi goma da ake gudanar da hada-hadar a kowane mako, wanda kuma suke da bukatar a yi musu garanbawu domin samar da saukin gudanar da yin hada-hada a cikinsu tare da kuma samar da tsaro.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI October 18, 2025 Noma Da Kiwo Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya October 11, 2025 Noma Da Kiwo Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe October 11, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnatin jihar da kuma kara da samar da

এছাড়াও পড়ুন:

An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna

Fargaba ta lulluɓe al’ummar Ungwan Nungu da ke gundumar Bokana a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna, bayan wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da mazauna yankin 11 a ranar Asabar yayin da suke dawowa daga gonakinsu.

Mazauna yankin sun ce an tare mutanen ne a wata hanyar daji da ke kusa da unguwar da yamma, inda aka tafi da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Lamarin ya tayar da hankula a ƙauyukan da ke kewaye, inda iyalai da dama suka kwana cikin fargaba.

Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu cewa wasu daga cikin waɗanda aka sace matasa ne da suka tafi gona domin yin roron wake lokacin da aka afka musu.

NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa

Ya ce: “An fara kai hari ne ga mutane 15, wasu sun tsere, wasu kuma aka sake su ba tare da sharaɗi ba. Amma har yanzu mutum 11 suna hannun ’yan bindiga, kuma sun buƙaci a biya su kuɗin fansa na naira miliyan biyar,” in ji shi.

Da yake tabbatar da afkuwar lamarin cikin wata sanarwa a ranar Talata, ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazavar Jama’a/Sanga, Hon. Daniel Amos, ya bayyana satar mutanen a matsayin mugunta da rashin tausayi, tare da yin Allah-wadai da kai hari kan talakawa masu aikin halaliya.

“Muna buƙatar kara tsaurara tsaro, yin amfani da dabarun bayanan sirri, da ɗaukar matakan gaggawa da haɗin gwiwa domin kwantar da hankalin jama’a da kuma ceto waxa0nda aka sace,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku