Isra’ila ta ce mashigar Rafah za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai abin da hali ya yi
Published: 19th, October 2025 GMT
Ofishin Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sanar a ranar Asabar cewa “Mashigar Rafah a Gaza za ta kasance a rufe har sai abin da hali ya yi a nan gaba.”
Ofishin Netanyahu ya kara da cewa, bude mashigar ya dogara ne bisa ga yadda Hamas ta aiwatar da tsarin yarjjeniyar da aka cimmawa wajen mika gawawwakin Isra’ilawa da ke hannunta.
Wannan bayanin ya zo ne jim kadan bayan da ofishin jakadancin Falasdinu a Masar ya sanar da cewa za a sake bude mashigar Rafah da ke kudancin zirin Gaza a ranar Litinin mai zuwa.
A nata bangaren, kungiyar Hamas ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, matakin da Netanyahu ya dauka yana a matsayin keta sharuddan yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da kuma karya alkawuran da ya dauka ga masu shiga tsakani da masu bayar da lamuni ga yarjejeniyar.
Kungiyar ta yi bayanin cewa, ci gaba da rufe mashigar Rafah, da hana fitar da wadanda suka jikkata da marasa lafiya, da hana shigar da kayan aiki na musamman da ake bukata domin neman wadanda suka bace a karkashin baraguzan gine-gine, hakan zai haifar da jinkirin dawo da gawarwakin Isra’lawan.
Kungiyar ta yi kira ga masu shiga tsakani da masu bayar da lamuni ga yarjejeniyar da su dauki matakin gaggawa don matsa lamba a kan Isra’ila domin bude mashigar Rafah cikin gaggawa, tare da tilasta mata yin aiki da dukkanin sharuddan da ke cikin yarjejeniyar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Bayyana Cewa: Kuduri Mai Lamba 2231 Ya Zo Karshe October 18, 2025 Kasashen Iran, Rasha, Da China Sun Jaddada Rashin Halaccin Dawo Da Tsohon Takunkumi Kan Iran October 18, 2025 Masani Kan Harkokin Tsaro Ya Ce: Makami Mai Linzamin Iran Kirar Ghadir Ya Aike Da Sako Ga Isra’ila October 18, 2025 Jami’in Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce: An Rusa Gaza Gaba Daya October 18, 2025 Joseph Kabila Ya Koma Kasarsa Domin Kalubalantar Hukuncin Kisa Da Aka Yanke Kansa October 18, 2025 Gaza Ta Bukaci A Binciki Isra’ila Kan Sace Sassan Jiki A Gawarwakin Falasdinawa October 18, 2025 Hamas Ta Bukaci A Kafa Kotun Kasa Da Kasa Kan Gawarwarkin Da Isra’ila Ta Dawo Mata Da Su. October 18, 2025 Madagascar : An rantsar Da Michael Randrianirina A Matsayin Shugaban Kasar October 18, 2025 Iran Ta yi Tir Da Harin da Isra’ila Ta kai Kudancin Kasar labanon. October 18, 2025 Majalisar Dattawa Za Ta Gana Da Ministan Ilimi Kan Batun Yajin Aikin Asuu. October 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: mashigar Rafah
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta Bukaci A Kafa Kotun Kasa Da Kasa Kan Gawarwarkin Da Isra’ila Ta Dawo Mata Da Su.
A wani bayani da kungiyar Hamas din ta fitar tayi tir da Israila kan yanayin da gawarwarakin da ta bata na palasdinawa dake hannunta, inda aka ga alamomi na Azabtarwar ajikinsu da kuma cire wasu sassan jikinsu don haka ta yi kara da a kafa kwamitin bincike na kasa da kasa kan halin rashin dan adamta da isra’ilan ta nuna kan gawarwakin.
Ta ce yin amfani da hanyoyi daban daban wajen Azabtarwa yana haifar da damuwa sosai kuma ya taka dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar Janeva, kuma wadannan ayyukan daidai suke da kisan kiyashi kan alummar falasdinu,
Wasu kungiyoyin sun mika batun ga kwamitin kula da hakokin dan adam na majalisar dinkin duniya domin yin matsin lamba kan isra’ila don a gudanar da bincike,
Kungiyar hamas ta ce tana kira ga kunyoyin kare hakkin bil adama da na kasa da kasa da su rubuta wannan abin da ya faru, kuma a gudanar da bincike na gaggawa tare da gurfanar da shuwagabannin isra’ila kan laifukan cin zarafin bil adama da ba’a taba ganin irinsa ba a tarihi na zamani.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Madagascar : An rantsar Da Michael Randrianirina A Matsayin Shugaban Kasar October 18, 2025 Iran Ta yi Tir Da Harin da Isra’ila Ta kai Kudancin Kasar labanon. October 18, 2025 Majalisar Dattawa Za Ta Gana Da Ministan Ilimi Kan Batun Yajin Aikin Asuu. October 18, 2025 Gaza ta bukaci a binciki Isra’ila kan sace sassan jiki a gawarwakin falasdinawa October 18, 2025 Madagaska : An rantsar da Kanar Randrianirina a matsayin shugaban kasa October 18, 2025 Al-Houthi: Matsin lamba bai hana Iran ci gaba da goyon bayan Falasdinu ba October 18, 2025 Marzieh Jafari Ta Dauki Lambar Yabo Ta Horar Da Mata Wasan Kwallon Kafa Ta Nahiyar Asia October 18, 2025 Iran: Kudurin Kwamitin Tsaro Kan Yarjeniyar JCPOA Ya Kawo Karshe A Yau October 18, 2025 Iran: Kauyuka 3 Sun Shiga Cikin Wuraren Bude Ido Na Duniya October 18, 2025 Aref: Kofar Tattaunawa A Bude Take, Amma Ba Zamu Amince Da Bukatun Da Basa Da Ma’an Ba October 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci