Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 159
Published: 19th, October 2025 GMT
159-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan na Aya. Shahid Murtadha Muttahari, ko cikin littafin Mathnawi na maulana jalaluddeen Rumi ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da a mu a cikin shirimmu na yau.
////…Madalla. Masu sauraro a cikin shirimmu da ya gabata a kuma cikin sirar Imam Al-Hassan (a) dan Fatimah (s) diyar manzon All..(s) da muke kawo mako, a cikin shirimmu da ya gabata. Mun kawo maku wasikar da Imam Al-Hassan(a) ya rubutawa Mu’awiya dan Abu Sufyan wanda yayi tawaye wa mahaifinsa imam Ali(a) bayan an masa ba’a a madina da sunan neman jinin Khalifa uthman. Don haka Imam Alhassan ya gaji mahaifi a wannan jayayyar, ya bukaci Mu’awiya ya dawo ya mika kai ya hada kan musulmi.
Kafin haka Imam Al-hassan ya tunatar da shi abubuwan da suka faru bayan wafatin manzon Allah (s) ta yadda musulmi larabawa suka fara jayayya a tsakaninsu kan wanda zai karbi shugabancin Muhammad (s) a bayansa. Bayan jayayya mai yawa sai mutanen ansar suka barwa muhajirun wadanda kuma kuraishawa ne. suka yi bai’a wa Khalifa na farko.
Ya kuma tabbatar da cewa kuraishawa sun zalunci ahlulbaiti a lokacinda suka ki mayar masu da hakkinsu bayan sun bukaci hakan.
Sannan munji yadda kafin Imam Al-Hassan (a) mahaifinsa Amirulmuminina Aliyu dan Abitalib (a) ya kawo wannan batun a cikin wasikar da ya rubutawa mutanen kasar Masar bayan ya karbi khalifanci inda, yad aga bayyana wannan al-amarin, kan cewa kuraishawa sun kwace hakkinsa, na shugabanci, duk da cewa kafin wafatin manzon All..(s) bai tsamman zasu yi haka. Amma da suka yi kuma shi yaki ya bisu, amma da ya ga cewa abinda suka yi yasa larabawa suka ridda su fice daga addinin musulunci, suna ma kira ga rusa addinin Mohammad (s), sai ya ga cewa dolene ya taimakawa musulunci da musulmi don kada musibun su yi masa yawa, idan musulunci ya rushe ko ya sami tawaya.
A cikin shirimmu nay au zamu fara kawo maku wasikar Mu’awiya dan Abu Sufyan bayan ya karbi ta Imam Alhassan ya kuma karantata. Inda yake cewa
(Bayan haka. Hakiki na fahinda abinda ka fada dangane da manzon Allah (s) shi ne ya fi cancanta falala gaba daya daga na farko zuwa na karshe, sannan ka ambaci jayayyar musulmi kan shugabanci a bayansa, ka kuma bayyana tuhumarka ga Abubakar Assidiku da Umar, da kuma Abu Ubaida dan Jarrah amintacce, da salihan bayi cikin wadanda suka yi hijira, ban ji dan kayi haka ba. Don lalle a lokacinda al-umma ta yi jayayya kan shugabanci a tsakaninta, ta ga cewa kuraishawa ne suka fi cancanta da lamarin, sai kuraishawa da Ansar da masu falala a cikin addini daga cikin musulmi suka ga cewa zasu shugabantar da wanda ya fisu ilmi a cikinsu, kuma basu yi kuskure ba, don da sun san wani mutum wanda ba Abubakar ba, wanda zai kare hurumin addinin musulunci, da basu barshi suka zabi Abubakar ba.
Sannan a yau indan mun dawo Tsakani na da kai, al-amarin yana nan kamar yadda suka kasance, da na san cewa kai ne mafi sanin al-amuran shugabanci, kuma ka fi dacewa da shugabancin wannan al-ummar, kuma ka fi kyautata shugabanci, ka fi iya kaidi wa makiya, ka fi iya tara haraji, da na mika maka shugabanci bayan mahaifinka. Sannan mahaifinka ya yi makirci wa Uthman har aka kashe shi yana matsayin wanda aka zalunta, sai Allah ya nemeshi da jininsa, wanda Allah ya neme shi da wani abu ba zai kubuce masa ba, sannan ya kwacewa al-umma al-amarin shugabancinta, ya rarraba hadin kanta, sai wadanda suke dai-dai da shi a matsayi a cikin wadanda suke da sabika a shiga musulunci, da yin jihadi, da kuma dadewa a cikin musulunci, suka saba masa, yayi iddi’a’ii kan cewa sun kwance bai’arsa, ya yakesu ya kuma zubar da jinni, ya kuma halatta huruminsu, sannan ya zo mana yana iddi’a ‘iin bai’arsa a kammu, amma yana son ya mulke mu ne a dole, mun yakeshi ya yake mu. )
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Hassan(a) 158 October 19, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Al-Hassan (a) 157 October 19, 2025 KissoshinRayuwa : Sirar Imam Al-Hassan(a) 156 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 155 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 154 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 153 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 152 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 151 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 150 October 19, 2025 Wata Kotun A Murka Ta Haramtawa HKI Kafa Na’urorin Leken Asiri A Wayoyi Masu WattsApp October 19, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
KissoshinRayuwa : Sirar Imam Al-Hassan(a) 156
156-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littana wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Murtadha Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawa, na maulana jalaluddeen Rumi ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.
////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Hassan Al-Mujtaba(a) dan Fatimah diyar manzon All..(s) da muke kawo muku. Mun yi maganar yadda, yadda Mu’awiya dan abusufyan ya kidemi bayan bayan ya sami labarin cewa an yiwa Imam Hassan bai’a a matsayin Khalifan musulmi a kufa, sannan ya kira taron mashawartansa suka zauna suka kuma fidda wassu al-amura guda biyu don fuskantar Imam Al-Hassan(a). Kuma sune, aika jasusu mai aiko masu labarai sirri daga kasar Iraki, musamman a biranen Kufa da Basra wadanda suka kasance manya-manyan garuruwan a lokacin a kasar Iraki.
Sannan na biyu kuma suna son sayan wasu manya-manyan shugabannin Iraki wadanda suke taimakawa Imam Alhassan (a) don su barshi shikadai, hakan zai tilasta masa ya mika kai ga mu’awiya dan Abusufyan.
Sannan ba tare da bata lokaci ba suka aika mutanen biyu zuwa kasar Iraki, daya a Basra da kuma a Kufa babban birnin daular musulunci karkashin Imam Hassan (a).
A lokacin da wadan nan ma’aikata biyu suka je inda aka turasu suka fara ayyukansu na leken asiri, sai asirinsu ya tonu, Imam Hassan (a) ya tura shurdatul Khamis suka bazu a cikin kufa har sai da suka zakulo jasusun Ma’awiya a cikin birnin suka kawoshi a gaban Imam Alhassan (a) wanda ya bada Umurni a kashe sai aka kashe shi.
Haka ya faru a Basra ma, inda Abdullahi dan Abbas ® ya sa aka nemo shi aka kuma kama shi aka kawo shi a gabansa ya bada umurni aka kasheshi.
Daga sai Imam Hasan (a) ya rubutawa Mu’awiya wasika, inda a ciki ya aibata shi da cusa dan leken asiri a cikin kufa da Basar, sannan yayi masa barazana da yaki. Sannan ya fada masa cewa ya ji labarin ya nuna jin dadi da shahadar mahaifinsa Imam Ali (a).
Mu’awiya ya tsorata ya kuma mayar masa da amsa kan cewa bai ji dadin kasan mahaifinsa ba, amma yaki ya yi magana kan dan leken asirin da ya aika. Haka ma Ibnu Abbas ya rubutawa Mu’awiya wasika yana aibata shi da cusa dan leken asiri a cikin mutanen Basra. Shi ma mu’awiya ya mayar masa da amsa inda ya bayyana masa cewa Imam Alhassan (a) ya rubuta masa wasika irin tasa, yana aibata shi. Amma bai bayyanawa Ibn Abba kan cewa Imam Al-Hassan (a) yayi masa barazana da yaki.
Bayan haka sai Ibn Abbas ya rubutawa Imam Alhassan wasika inda a cikin yake bashi shawara yake kuma kodaitar da shi kan yakar Mu’awiya da kuma wasu dabarbaru da ya bashi. Ga nassin wasikar kamar yadda take.
:Bayan haka, Lalle musulmi sun mayar maka shugabancinsu bayan Aliyu (a), to zage dantse don yaki, ka yi jihadi da makiyinka, ka kusanto da mutanenka, wadanda suke da raunin Imani ka sayi addininsu don kare kanka daga cutar da kai. Ka kuma dora mutane daga manya-manyan gidaje da daukaka don sai danginsu su bika sannan kan jama’a ta hadu, …..
Ka yi koyi da abinda abinda ya zo daga wajen shuwagabanni adilai, suna cewa karya bata halatta sai a yaki… kuma ka san cewa abinda ya sa mutane suka kauracewa mahaifinka suka koma wajen Mu’awiya shi ne shi mai son daidaita rabo a tsakanin, sai wannan yayi masu nauyi.
Kuma ka san cewa kana yakar wanda ya yaki All..da manzonsa(a) a farkonmusulunci ne, har sai da al-amarin All..ya bayyana ya kuma sami rinjaye. A lokacinda aka kadaita Allah aka shafe shirka addini ya daukaka, sai suka bayyana cewa su masu Imani ne a gaban mutane, suka karanta Alkur’ani suna masu istahza’I da ayoyinsa, suka tsaida sallah suna cikin kasala, suna aikata sauran farillu ba da sonsu ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 155 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 154 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 153 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 152 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 151 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 150 October 19, 2025 Wata Kotun A Murka Ta Haramtawa HKI Kafa Na’urorin Leken Asiri A Wayoyi Masu WattsApp October 19, 2025 Sojojin Najeriya: Rahotanni Dangane Da Juyin Mulki Wa Shugaba Tinubu Ba Gaskiya Bane October 19, 2025 Hamas Ta Gabatar Da Sunayen Kwararrun Da Zasu Gudanar Da Harkokin Gaza October 19, 2025 Doha: Pakistan da Afghanistan sun amince da tsagaita bude wuta a tsakaninsu October 19, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci