Hamas Ta Gabatar Da Sunayen Kwararrun Da Zasu Gudanar Da Harkokin Gaza
Published: 19th, October 2025 GMT
Wani babban jami’in kungiyar Hamas a Gaza ya bada sanarwan cewa, kungiyarsa ta gabatar da sunayen mutane fiye da 40 wadanda yan kasa ne kuma kwarraru, don sanyasu a mukaman harkokin gudanarwan zirin gaza.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Muhammad Nazal, wani babban jami’I na kungiyar yana fadawa tashar talabijin ta Aljazeerah na kasar kasar Qatar haka, a wata hirar da ta hada su a jiya Asabar.
Nazal ya kara da cewa, wadannan masana kuma kwararru a harkokin gudanarwa za su taimaka wajen ganin an gabatarwa mutanen Gaza ayyukan jinkai don fidda Falasdinawa a Gaza daga mummunan halin da suke ciki a bangarori daban daban na rayuwa.
Kimanin wata guda da ya gabata ne kungiyar ta bada sanarwan cewa zata mika harkokin gudnarwa na zirin gaza ga wasu falasdinawa kwararru wadanda zasu gudanar da harkokin a gaza, bisa shawarar da shugaba Trump ya bayar danagne da tsagaita wuta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Doha: Pakistan da Afghanistan sun amince da tsagaita bude wuta a tsakaninsu October 19, 2025 Isra’ila ta ce mashigar Rafah za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai abin da hali ya yi October 19, 2025 Araqchi: Kuduri Mai Lamba 2231 Ya Zo Karshe October 18, 2025 Kasashen Iran, Rasha, Da China Sun Jaddada Rashin Halaccin Dawo Da Tsohon Takunkumi Kan Iran October 18, 2025 Masani Kan Harkokin Tsaro Ya Ce: Makami Mai Linzamin Iran Kirar Ghadir Ya Aike Da Sako Ga Isra’ila October 18, 2025 Jami’in Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce: An Rusa Gaza Gaba Daya October 18, 2025 Joseph Kabila Ya Koma Kasarsa Domin Kalubalantar Hukuncin Kisa Da Aka Yanke Kansa October 18, 2025 Gaza Ta Bukaci A Binciki Isra’ila Kan Sace Sassan Jiki A Gawarwakin Falasdinawa October 18, 2025 Hamas Ta Bukaci A Kafa Kotun Kasa Da Kasa Kan Gawarwarkin Da Isra’ila Ta Dawo Mata Da Su. October 18, 2025 Madagascar : An rantsar Da Michael Randrianirina A Matsayin Shugaban Kasar October 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
A mafi yawan ƙasashen duniya, ana ɗaukar jakadu a matsayin fuskar ƙasa kuma ginshiƙan hulɗar diflomasiyya. Saboda haka, akwai muhimman halaye da suke tilas jakadan ƙwarai ya mallaka domin ya wakilci ƙasarsa cikin mutunci, da nagarta da kwarewa.
Tun bayan da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fitar da sunayen jakadu da yake sa ran majalisar kasa ta tantance ne dai batun ke ta shan suka daga manazarta kan sunayen da ya fitar.
Ko wadanne irin halaye ya kamata jakada ya mallaka a yayin da za a tura shi a matsayin wakili a wata kasa?
NAJERIYA A YAU:Waiwaye Kan Irin Gudunmawar Da Sheikh Dahiru Bauci Ya Bayar Ga Cigaban Addini DAGA LARABA: Shin Ya Kamata A Biya Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan