Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Published: 19th, October 2025 GMT
An saki ɗan jarida, Ibrahim Ɗan’uwa Rano, bayan da ƴansanda suka tsare shi a shalƙwatar Rundunar Ƴansanda ta Zone 1 Kano bisa zargin batanci ga wani mutum.
Sakin nasa ya biyo bayan suka da matsin lamba daga ƙungiyoyin fararen hula irinsu Cibiyar Fasahar Bayanai da Ci Gaban Jama’a (CITAD), da Amnesty International, da sauran ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam, waɗanda suka bayyana tsarewar tasa a matsayin mataki na keta haƙƙin ɗan Adam da kuma yunƙurin danne ƴancin ƴan jaridu.
Ƙungiyoyin sun buƙaci a sake shi ba tare da wani sharaɗi ba, suna mai cewa tsarewar ta saɓawa dokar kundin tsarin mulkin Nijeriya da kuma ƙa’idojin kare ƴancin ƴan jarida na ƙasa da ƙasa.
Sun kuma yi kira ga hukumomin tsaro da su daina amfani da ƙarfin gwamnati wajen tsoratarwa ko hana ƴan jarida yin aikinsu cikin gaskiya da riƙon amana.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: Ɗan Jarida
এছাড়াও পড়ুন:
Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
Abin da ya rage yanzu shi ne za a zuba ido don ganin irin sauyin da zai kawo na tsaro a birnin tarayyar, sakamakon taɓarɓarewar tsaro da ya addinin garin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA