Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU
Published: 18th, October 2025 GMT
Ya ce “Daga wancan lokacin zuwa yanzu, mun rasa Farsesoshi 309,wasu sun je Jami’oi masu zaman kansu a Nijeriya, sauran wasu sun je London, Saudi Arebiya, Kameroon da kuma wasu kasashe.Kwarrunmu wadanda babban jari ne suna barin aiki saboda sharuddan aikinsu babu wani abin jin dadin da zai sasu ci gaba da kasancewa wuraren aikinsu na koyarwa kamar yadda ya ce,”.
Sabo ya bayyana cewa kungiyar za ta fara yajin aikin mako biyu daga ranar Litinin, idan har gwamnatin tarayya ta ci gaba watsi da maganar bukatunta da kuma inganta masu sharuddan aiki.
“Mun yi shiru har abin ya wuce misali.Hakkin mune nu ceto jami’oin gwamnati. Idan har gwamnati ta ci gaba da yin biris da mu, ba zamu ci gaba da sa ido ba yayin da lamarin ilimi yana kara durkushewa.
“Da muka bada wa’adin mako biyu, gwamnati ta farakiran waya ne, daganan suka fara kiran kungiyoyi kamar na makarantun fasaha, da Kwalejojin ilimi domin su kara dagula lamarin cewar akwai wani kokarin da ake na kawo matsala samar da matsaloli kan kasafin kudin ilimi domin dakushe irin gwagwarmayar samun bukatunsu da suke kamar yadda ya yi zargi,”.
Tun farko ne Shugaban kungiyar na ASUU-UDUS, Farfesa. Muhammad Almustapha, ya ce taron an kira shi ne domin a sanar da ‘yan Nijeriya dangane da irin koma bayan da ake samu a ilmin Jami’oi, da kuma gazawar gwamnati ta cika ma kungiyar alkawuran data yi.
“Shekarun da suka gabata, kungiyar ASUU ta saba da tafiye- tafiye yajin aiki, saboda yana da matukar wuya gwamnati ta cika alkawuran da ta yi. Abin ya zama alkawari bias wani alkawarin da, ba za’a cika ba duk kuma wani tunanin da kungiyar take abin ya zama kanzon Kurege kama yadda ya jaddada”.
Kungiyar ta yi kira da gwamnati ta dauki mataki na gaggawa domin ta kawo karshe karshen yadda kwararru suke barin aikin koyarwa, domin a shawo kan kara lalacewar ilimin jami’a a Nijeriya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: gwamnati ta
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
’Yan bindiga sun harbe wata tsohuwa har lahira a wani sabon hari da suka kai ƙauyen Yankamaye da ke Ƙaramar Hukumar Tsanyawa a Jihar Kano.
Sun kai harin ne a daren ranar Asabar, a lokacin da mutanen ƙauyen ke kwance.
Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32Yayin kai harin, ’yan bindigar sun kuma sace aƙalla mutum uku.
Yankamaye, wani ƙaramin ƙauyen manoma ne, ’yan bindiga da ke tserewa daga maƙwabtan jihohin Kano ne suka fara kai musu hare-hare.
Kakakin rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an tura jami’ai domin bin diddigin maharan.
Mazauna ƙauyen sun ce ’yan bindigar sun isa ne a kan babura inda suka ajiye su daga nesa, sannan suka shiga ƙauyen a ƙafa.
A yayin taron majalisar zartarwa da aka gudanar kwanan nan, Gwamna Abba Yusuf, ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na magance matsalar tsaro.
Ya kuma ce hare-haren ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane, da ɓarayi shanu a wasu yankunan Arewacin jihar, babban abin damuwa ne.
Gwamnan, ya ce suna aiki tare da hukumomin tsaro don magance barazanar da kuma tabbatar da zaman lafiya.
Ya bayyana ƙananan hukumomin da abin ya shafa; Kunchi, Tsanyawa, Gwarzo, Kabo, Sumaila, Shanono, Tudun Wada, Doguwa, da Rogo.
Amma ya ce hukumomi na ci gaba da ayyuka domin toshe hanyoyin shigowar ’yan bindiga da kuma kare al’ummomin ƙauyuka.
“Duk da wasu ƙalubale da ake fuskanta a nan da can, jama’a su kwantar da hankalinsu, gwamnati tana aiki domin magance duk wata barazana ga zaman lafiya,” in ji Yusuf.
Gwamnan, ya kuma goyi bayan matakin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, na ayyana dokar ta-ɓaci a harkar tsaro a faɗin ƙasar nan.