Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano
Published: 19th, October 2025 GMT
Mahukunta sun kai samame tare da rufe wani gidan shan Shisha da ke kan titin Abdullahi Bayero a cikin ƙwaryar birnin Jihar Kano.
Bayanai sun ce wata rundunar haɗin gwiwa ce ta kai samamen da ta ƙunshi jami’an ukumar Kula da Yawon Buɗe Ido da kuma na Hukumar Hana Sha da Fataucin Ƙwayoyi (NDLEA) reshen Jihar Kano, da Hukumar ’Yan Sanda a Jihar Kano.
Wannan na cikin wata sanarwa da Hukumar Yawon Buɗe Ido ta Jihar Kano ta fitar a ranar Asabar, inda ta ce jami’an NDLEA sun kama wasu kayan maye da kuma wasu mutane da ake zargi da shaye-shaye a wurin.
Hukumar ta ce wannan aikin wani bangare ne na yunƙurin gwamnati a fagen yaƙi da matsalar shaye-shaye da kuma ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a ko’ina a faɗin jihar.
Shugaban Hukumar Yawon Buɗe Ido ta Jihar Kano, Alhaji Tukur Bala Sagagi ya jaddada cewa akwai dokar hana shan shisha a Jihar Kano, don haka gwamnati ba za ta lamunci karya wannan doka ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano a Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Za a kafa kamfanin ƙera kayan sola a Kano
Gwamnatin Jihar Kano ta ce nan ba da jimawa ba za a fara ƙera fanel da sauran kayayyakin samar da wutar lantarki daga hasken ranar a jihar.
Hakan a cewar gwamnatin ya biyo bayan samun masu zuba jari a fannin na makamashi, bayan rattaba hannu kan yarjejeniya da kamfanoni biyu da suka shahara a fannin, wato Tricell Solar Solutions da IRS Green Energy..
’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano Ka da a ɗora wa Tinubu laifin rikicin da ke faruwa a PDP — FayoseAn kulla yarjejeniyar ne tare da haɗin gwiwar Hukumar Wutar Lantarki ta Karkara (REA) domin bayar da shawarwari na fasaha da daidaita ayyuka, a yayin taron Sabunta Makamashi na Najeria (NERIF) na 2025 da aka gudanar a ranar Talata a birnin Abuja, kamar yadda mai magana da yawun Gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya bayyana.
Ya ce shugaban hukumar Zuba Jari ta jihar (Kan-Invest), Naziru Halliru ne ya jagoranci ƙulla yarjejeniyar a madadin Gwamna Abba Kabir Yusuf.
Sansusi ya ce ƙulla yarjejeniyar na cikin manyan matakai da gwamnatin ke ɗauka domin faɗaɗa samar da makamashi mai tsafta da araha, bunƙasa masana’antu a cikin gida, da samar da ayyukan yi ga al’ummar jihar.
Sanarwar ta kuma ce a karkashin wannan tsarin, kamfanin IRS Green Energy zai gina masana’antar kera kayan amfani da hasken rana da ke da ƙarfin samar da 600MW a shekara, yayin da Tricell Solar Solutions zai kafa wata da ke da ƙarfin 500MW, lamarin da ya ce zai mayar da Kano cibiyar samar da sabon makamashi a yankin.