Leadership News Hausa:
2025-10-19@10:48:01 GMT

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

Published: 19th, October 2025 GMT

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

Yanzu kuma za a ci gaba da tattaunawa kan yadda za a aiwatar da sauran sharuddan da ke ke kunshe a yarjejeniyar.

 

Masu sanya ido na ganin cewa aikin sake ginan yankin Gaza wanda aka rushe kusan daukacinsa a yakin da aka yi na shekara biyu, zai zama babban kalubale.

 

Wannan ce ranar da kowa ke jira -Trump

A lokacin da Donald Trump ya yi jawabi, ya bayyana yau a matsayin “ranar da kowa ya yi ta hankoro da addu’ar ganin zuwan ta.

Shugaban na Amurka ya ce “Wannan yarjejeniya mai matukar tarihi” wadda gungun shugabannin duniya suka sanya wa hannu, na nuna cewa “addu’ar miliyoyin al’umma ta karbu”.

Daga nan sai ya ce shugabannin sun samu nasarar tabbatar da “zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya”, sannan ya taya kowa murna.

Haka nan Trump ya gode wa shugaban Masar Abdul Fattah al Sisi bisa karrama shi da lambar girmamawa ta kasar ta ‘Order of the Nile’.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani October 19, 2025 Manyan Labarai ‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi October 19, 2025 Da ɗumi-ɗuminsa DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki October 18, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama ɓarayi da motocin da aka sace a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta samu nasarar gano wasu motoci da aka sace tare da kama wasu da ake zargin ɓarayi ne masu aikata laifuka ciki har da ƙwace bindiga ƙirar gida.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a madadin Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar, CP Bello Yahaya, inda ya ce nasarorin sun biyo bayan sintiri da sahihan bayanan leƙen asiri da haɗin gwiwar al’umma.

Miyetti Allah ta dakatar da shugabanninta a jihohi 3 An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi

A cewar sanarwar, a ranar 13 ga Oktoba, 2025, jami’an sashin Balanga sun gano wata mota ƙirar Toyota Jeep launin baƙi da lambar rijista ABUJA, ABC 241 DW a hanyar Bangu–Laura a Ƙaramar hukumar Balanga

Barayin motar sun yi ƙoƙarin tsere wa bayan ganin ’yan sanda, inda suka kai wa jami’ai hari da ƙaramar bindiga ƙirar gida kafin su bar motar suka gudu da babur.

Bincike ya gano takardun motoci biyu ƙirar Lexus, kuma daga baya aka tabbatar cewa motar asali Lexus Jeep ce mai launin toka da aka sake launinta kamar Toyota Prado, wadda aka sace daga Abuja a ranar 5 ga Oktoba.

Rundunar ta ce, tana aiki da rundunar Abuja don kamo waɗanda suka tsere.

Haka kuma, a ranar 15 ga Oktoba, 2025, ’yan sanda daga sashin Gombe sun kama Sani Bappari, mai shekara 45 daga unguwar Mallam Inna, bisa zargin satar mota ƙirar Honda Civic da lambar rijista DKU 564 AA, wadda aka sace a tsakiyar gari

An same ta a hannunsa kuma yanzu haka tana hannun ’yan sanda a matsayin shaida.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama sojoji 20 kan yunƙurin kifar da gwamnatin Tinubu
  • HOTUNA: Al’ummar Jihar Neja sun yi addu’o’in neman zaman lafiya
  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro
  • Taron Malamai Ya Nemi Haɗin Kai Domin Magance Rashin Tsaro, Talauci Da Rarrabuwa A Arewa
  • Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
  • Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya
  • FMC Birnin Kudu Ya Yi Bikin Ranar Maganin Kashe Radadi Ta Duniya
  • An kama ɓarayi da motocin da aka sace a Gombe
  • Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu