Aminiya:
2025-10-19@01:08:48 GMT

An tsinci gawar wata mata da aka yi wa kisan gilla a Yobe

Published: 19th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta gano gawar wata mata mai suna Falmata Abubakar, mai kimanin shekaru 45, wadda aka yi wa kisan gilla a garin Gashuwa, kusa da Jami’ar Tarayya Gashuwa (FUGA), a Ƙaramar Hukumar Bade.

Rundunar ta samu labarin ne da safiyar ranar Asabar, 17 ga watan Oktoba 2025, misalin ƙarfe 7 na safe.

An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano Wasu jiga-jigan ADC za su dawo jam’iyyarmu — Shugaban APC

Wani mutum mai suna Yusuf Sarkin Baka, mazaunin unguwar Sabon Daula ne, ya gano gawar a kusa da jami’ar.

Bayan samun rahoton, ’yan sanda daga ofishin Gashuwa sun ziyarci wajen, inda suka tabbtar marigayiyar mazauniyar Abasha, unguwar Sarkin Hausawa a Gashuwa.

An same ta sanye da baƙin hijabi.

An kai gawarta Asibitin Ƙwararru na Gashuwa, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarta.

Daga baya sun miƙa wa iyalanta gawar domin yi mata jana’iza bisa tsarin addinin Musulunci.

Bincike ya nuna cewa, an jefar da gawar matar ne kilomita biyu daga gidanta.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado, ya tabbatar da cewa rundunar za yi bincike domin gano waɗanda suka aikata laifin.

Ya kuma buƙaci jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da bai wa rundunar haɗin kai wajen gano masu hannu a lamarin.

Rundunar ta jaddada ƙudirinta na kare rayuka da dukiyoyi, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Gawa Wata mata

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

 

Haka kuma, shugabar kasar Iceland Halla Tomasdottir ta ce, a matsayin wata babbar kasa, kiran da kasar Sin ta yi yana da muhimmanci ga sauran kasashen duniya. Ayyukan da kasar Sin ta yi a fannin tabbatar da ci gaban mata da daidaiton jinsi, sun kasance abin koyi ga kasashen duniya.

 

Bugu da kari, shugabar kasar Dominica Sylvanie Burton, ta ce jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi a yayin taron kolin mata na duniya, ya samar da sabon karfi ga raya ci gaban mata bisa dukkan fannoni, kuma kasarta na fatan ci gaba da yin hadin gwiwa da kasar Sin a fannoni da dama. (Mai Fassara: Maryam Yang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori October 16, 2025 Daga Birnin Sin Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan October 15, 2025 Daga Birnin Sin Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji  October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tsinci gawar wata mata a kusa da Jami’ar Tarayya a Yobe
  • Sojoji sun tallafa wa mutanen Yobe da N23m bayan harin kuskure
  • JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i
  • Ma’aurata 136 sun kashe juna a shekara 4
  • Yadda ma’aurata 136 sun kashe juna a shekara 4
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Kafa Dokar Wuraren Tsaro A Makarantu
  • ’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe
  • Za a biya tsofaffin ma’aikatan ƙananan hukumomi kuɗaɗe a Yobe
  • Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi