Aminiya:
2025-12-03@08:38:44 GMT

An tsinci gawar wata mata da aka yi wa kisan gilla a Yobe

Published: 19th, October 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta gano gawar wata mata mai suna Falmata Abubakar, mai kimanin shekaru 45, wadda aka yi wa kisan gilla a garin Gashuwa, kusa da Jami’ar Tarayya Gashuwa (FUGA), a Ƙaramar Hukumar Bade.

Rundunar ta samu labarin ne da safiyar ranar Asabar, 17 ga watan Oktoba 2025, misalin ƙarfe 7 na safe.

An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano Wasu jiga-jigan ADC za su dawo jam’iyyarmu — Shugaban APC

Wani mutum mai suna Yusuf Sarkin Baka, mazaunin unguwar Sabon Daula ne, ya gano gawar a kusa da jami’ar.

Bayan samun rahoton, ’yan sanda daga ofishin Gashuwa sun ziyarci wajen, inda suka tabbtar marigayiyar mazauniyar Abasha, unguwar Sarkin Hausawa a Gashuwa.

An same ta sanye da baƙin hijabi.

An kai gawarta Asibitin Ƙwararru na Gashuwa, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarta.

Daga baya sun miƙa wa iyalanta gawar domin yi mata jana’iza bisa tsarin addinin Musulunci.

Bincike ya nuna cewa, an jefar da gawar matar ne kilomita biyu daga gidanta.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Emmanuel Ado, ya tabbatar da cewa rundunar za yi bincike domin gano waɗanda suka aikata laifin.

Ya kuma buƙaci jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da bai wa rundunar haɗin kai wajen gano masu hannu a lamarin.

Rundunar ta jaddada ƙudirinta na kare rayuka da dukiyoyi, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Gawa Wata mata

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026

Daga Usman Muhammad Zaria 

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ya zuwa yanzu ta mayar da sama da naira miliyan 50 ga maniyyatan jihar na shekarar 2026, biyo bayan rage kudin kujerar aikin Hajji da Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sanar.

Daraktan Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, an mayar da kudaden ga maniyyatan da suka riga suka biya kudin kujerunsu ga hukumar kafin a rage farashin.

Ahmed Labbo ya ce NAHCON ta sake fasalin kudin Hajj na Yankin Arewa wanda yanzu ya kai sama da naira miliyan 7 da dubu 600 yana mai jaddada cewa mayar da kudin umarni ne daga Hukumar Alhazai ta Kasa, sakamakon gagarumin ragin da aka yi wa kujerar Hajjin shekarar 2026.

Ya jinjina wa jami’an hukumar na yankuna bisa kwazon tattara takardun  zuwa Hajj da bayanan maniyyata cikin sauri.

Yayin da yake magana kan shirye-shiryen aikin Hajjin 2026, Labbo ya bayyana cewa hukumar na aiki ba dare ba rana domin tabbatar da ingantattun tsare-tsare ga tawagar jihar a ƙasar Saudiyya.

Ya kuma yi kira ga maniyyata su tabbatar sun biya kudin kujerunsu kafin ko a ranar 24 ga Disamba, 2025.

Ahmed Labbo ya bayyana godiya ga Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da jajircewarsa ga hukumar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Kalubalen Dake Gaban Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro
  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 12 da ɓacewarsu a Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno
  • ’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato
  • Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano