An bude taron sanin makamar aiki na kasa da kasa mai taken “Cika shekaru 80 da kafuwar MDD: Makomar tsarin duniya, dokokin kasa da kasa, da ra’ayin kasancewar bangarori da dama”, wanda jami’ar Wuhan ta kasar Sin, da jami’ar Benha ta kasar Masar suka hada kai suka karbi bakuncin shirya shi.

 

Yayin bude taron a yau Asabar a birnin Wuhan na kasar Sin, tsohon mataimakin sakatare-janar na MDD Miguel de Serpa Soares, da babban sakataren kungiyar ba da shawarwari kan shari’a ta Asiya da Afirka ko (AALCO) Dr.

Kamalinne Pinitpuvadol, da shugaban jami’ar Benha ta Masar Nasser EL-Gizawy, da farfesa a jami’ar Wuhan Ignacio de la Rasilla, da ma wasu mahalartan taron sun bayyana cewa, dole ne a kare sakamakon nasarar da aka cimma a yakin duniya na biyu, da kuma tsarin duniya da aka kafa bayan yakin yayin da ake tunawa da cika shekaru 80 da kafuwar MDD, da amincewa da gaskiyar tarihi da ta shari’a, wato Taiwan wani yanki ne na kasar Sin, wanda aka tabbatar a wasu takardun dokokin kasa da kasa, ciki har da “Sanarwar Alkahira”, da “Sanarwar Potsdam”, da kuma kuduri mai lamba 2,758 na babban taron MDD, kana da tsayawa kan ainihin ka’idoji na dokokin kasa da kasa, kamar daidaiton mulkin kai, da rashin tsoma baki cikin harkokin cikin gida da dai sauransu, da kuma nuna goyon baya ga MDD, don ta taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa, da ma aiwatar da ra’ayin cudanyar bangarori da dama bisa gaskiya. (Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya October 18, 2025 Daga Birnin Sin Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103 October 18, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai October 18, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Kafa Dokar Wuraren Tsaro A Makarantu

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta fara aiki kan dokar da za ta kafa wuraren tsaro (safe spaces) a makarantu domin karfafa ilimin yara mata a jihar.

Shugaban Kwamitin Ilimi, Honarabul Mahmud Lawal, ya bayyana hakan a babban taro kan Ilimin Yara Mata  da aka gudanar a Zariya, wanda Cibiyar Kula da Ilimin Yara Mata (CGE) ta shirya don tunawa da Ranar Yara Mata ta Duniya ta 2025.

Ya ce dokar, mai taken “Dokar Wuraren Tsaro a Jihar Kaduna, 2025,” za ta kare ‘yan mata daga cin zarafi, hana wariya, da samar da tsarin horaswa da rahoto a makarantu.

Daraktar CGE, Hajiya Habiba Mohammed, ta ce taron na da nufin kara karfafa ‘yan mata a matsayin shugabannin da za su kawo sauyi, musamman a lokacin rikice-rikice da suke fuskantar kalubale irin su aure da wuri da barin makaranta.

 

Ta ce cibiyarsu na ganin ilimi a matsayin makamin da zai bai wa ‘yan mata damar canza al’umma, kuma dokar majalisar za ta taimaka wajen tabbatar da shirye-shiryen su a makarantu.

A jawabinsa a wurin taron, Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Farfesa Adamu Ahmed, ya yaba da taken taron, yana mai cewa ya dace da kalubalen da ‘yan mata ke fuskanta.

Ya ce daya cikin kowanne ‘yan mata hudu a yankin na yin aure kafin shekaru 18, kuma har yanzu ba su da daidaiton damar ilimi kamar maza.

Farfesa Ahmed ya bayyana cewa ABU na kara yawan ‘yan mata da take karɓa, inda suka kai kashi 42 cikin 100, tare da kira ga gwamnati da masu ruwa da tsaki su kara zuba jari a ilimin ‘yan mata.

 

Ibrahim Suleiman

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
  • Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai
  • JIBWIS FCT Ta Yi Taron Yaye Iyaye Mata Da Suka Kammala Koyon Sana’o’i
  • Aref: Kofar Tattaunawa A Bude Take, Amma Ba Zamu Amince Da Bukatun Da Basa Da Ma’an Ba
  • Gwamnonin APC sun yi taro a Jihar Kebbi
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Kafa Dokar Wuraren Tsaro A Makarantu
  • ‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 
  • Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
  • Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona