An bude taron sanin makamar aiki na kasa da kasa mai taken “Cika shekaru 80 da kafuwar MDD: Makomar tsarin duniya, dokokin kasa da kasa, da ra’ayin kasancewar bangarori da dama”, wanda jami’ar Wuhan ta kasar Sin, da jami’ar Benha ta kasar Masar suka hada kai suka karbi bakuncin shirya shi.

 

Yayin bude taron a yau Asabar a birnin Wuhan na kasar Sin, tsohon mataimakin sakatare-janar na MDD Miguel de Serpa Soares, da babban sakataren kungiyar ba da shawarwari kan shari’a ta Asiya da Afirka ko (AALCO) Dr.

Kamalinne Pinitpuvadol, da shugaban jami’ar Benha ta Masar Nasser EL-Gizawy, da farfesa a jami’ar Wuhan Ignacio de la Rasilla, da ma wasu mahalartan taron sun bayyana cewa, dole ne a kare sakamakon nasarar da aka cimma a yakin duniya na biyu, da kuma tsarin duniya da aka kafa bayan yakin yayin da ake tunawa da cika shekaru 80 da kafuwar MDD, da amincewa da gaskiyar tarihi da ta shari’a, wato Taiwan wani yanki ne na kasar Sin, wanda aka tabbatar a wasu takardun dokokin kasa da kasa, ciki har da “Sanarwar Alkahira”, da “Sanarwar Potsdam”, da kuma kuduri mai lamba 2,758 na babban taron MDD, kana da tsayawa kan ainihin ka’idoji na dokokin kasa da kasa, kamar daidaiton mulkin kai, da rashin tsoma baki cikin harkokin cikin gida da dai sauransu, da kuma nuna goyon baya ga MDD, don ta taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa, da ma aiwatar da ra’ayin cudanyar bangarori da dama bisa gaskiya. (Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya October 18, 2025 Daga Birnin Sin Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103 October 18, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai October 18, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Benin

Sojoji a kasar Jamhuriyar Benin sun kifar da gwamnati a wani juyin mulki da suka sanar a ranar Lahadi.

Sojojin sun bayyana ne a gidan talabijin na kasar inda suka sanar da tsige Shugaban Kasa Patrice Talon da kuma rushe duk hukumomin kasar.

Dakarun, karkashin jagorancin Laftanar Kanar Pascal Tigiri, sun rufe iyakokin kasar da rushe jam’iyyun siyasa.

Zuwa lokacin kammala wannan labarin babu labarin halin da Shugaba Talon wanda ke kan karagar mulkin tun a 2016 yake ciki.

Amma ministan harkokin kasar, Olusegun Ajadi Bakari, ya ce an samu yunkurin kifar da gwamnati, amma ana neman shawo kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Benin
  • Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri
  • Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21
  • Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi
  • Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
  • ’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo
  • Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha