Aminiya:
2025-12-04@00:37:31 GMT

Matasa sun kama ɗan fashi ya kai hari gidan burodi a Kaduna

Published: 19th, October 2025 GMT

Wani ɗan fashi da makami ya kai hari wani gidan biredi da ke cikin garin Kafanchan, a Jihar Kaduna, inda ya harbi ɗaya daga cikin ma’aikatan gidan sannan ya yi yunƙurin tserewa da kuɗi masu yawa.

Manajan gidan burodin, Abdullahi Babiyo, ya bayyana cewa suna cikin aiki lokacin da ɗan fashin, ya shiga gidan da bindiga, inda ya yi barazanar harbi idan bai buɗe masa ƙofa ba.

An saki Ɗan Uwa Rano bayan tsare shi kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano Talauci ne babban maƙiyin ɗan Adam — Atiku

Ɗaya daga cikin ma’aikatan gidan da aka harba, Muhammad Abdulmumin, wanda yanzu haka yake jinya a asibiti, ya ce ɗan fashin ya shiga gidan fuskarsa a rufe da bindiga AK-47.

Ya ce kai-tsaye ya nufi inda suke ajiye kuɗi.

“Yana zuwa ya ce mu zuba kuɗin cikin jakar da ya zo da ita. Da muka fara gardama sai ya yi harbi sau biyu, harsashi ɗaya ya goge ni a ƙafa,” in ji Abdulmumin.

Sai dai matasan unguwar sun bi ɗan fashin a baya, inda suka kama shi yayin da yake ƙoƙarin tserewa da jakar kuɗin, sannan suka miƙa shi hannun ’yan sanda.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, bai amsa kiran wayar da aka masa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Fashi

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u 

’Yan bindiga kimanin guda huɗu dauke da makamai sun kai hari a garin Eruku da ke ƙaramar hukumar Ekiti a jihar Kwara, inda suka sace wani manomi mai suna Mista Aasaru.

Rediyon Najeriya ya ruwaito  cewa wannan hari shi ne na biyu da aka kai wa garin Eruku cikin wata guda, kuma ya faru ne kwanaki kaɗan bayan gwamnatin tarayya ta samu ’yantar da mambobin Cocin Christ Apostolic Church (CAC) 38 da aka yi garkuwa da su a yankin.

Majiyar da ta yi magana da Rediyon Najeriya ta ce ’yan bindigar sun farmaki Aasaru ne a wani daji da ke kan hanyar Koro.

Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sandan jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin.

A cewarta, jami’an ’yan sanda daga sashin Eruku sun karɓi korafi a ranar Lahadi cewa wasu mutane huɗu dauke da makamai sun kutsa wata gona a kan hanyar Koro, Eruku, inda suka sace wani Mista Aasanru mai shekaru 40.

Ejire-Adeyemi ta ce ana cigaba da ƙokari wajen ganin an kubutar da manomin da aka sace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi