Aminiya:
2025-10-20@07:46:11 GMT

NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?

Published: 20th, October 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tun bayan fara shari’ar Nnamdi Kanu a shekarar 2021 mutane da dama suke bayyana ra’ayoyinsu a kan sake shi ko a kyale shari’a ta yi halinta.

 

Hasali ma har zanga-zanga wasu ‘yan Najeriya suka kira don bayyana bukatar sakin shugaban na ‘yan aware.

NAJERIYA A YAU: Yadda Cire Darasin Lissafi Zai Taimakawa Dalibai Shiga Jami’a DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan ko ya dace a saki Nnamdi Kanu?

Domin sauke shirin, latsa nan

.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan awaren IPOB

এছাড়াও পড়ুন:

NIEPA Ta Jinjinawa UNICEF Bisa Kare Hakkokin Yara Na Samun Ilimi A Najeriya

Cibiyar Tsare-tsaren Harkokin Ilimi da Gudanarwa ta Kasa (NIEPA) ta yaba da kokarin Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) wajen kare hakkokin yara na samun ilimi a Najeriya.

Darakta Janar na Cibiyar, Dakta David Shofoyeke ne ya bayyana hakan yayin bude taron horaswa na kwanaki uku ga masu gudanar da shirye-shiryen ilimin yankuna (LESOP) a Dutse, babban birnin Jihar Jigawa.

Dakta Shofoyeke, wanda Dakta Grace Omiyale Babbar Malamar Horaswa da Bincike a Cibiyar ta wakilta, ya tabbatar da cewa cibiyar tana da cikakken kudiri na sauya tsarin ilimi a Najeriya.

Ya bayyana cewa, samar da cikakken tsarin ilimi na jiha da kuma tsarin aiwatar da shirye-shiryen ilimi na jihohi yana taimakawa jihohi wajen tsara burinsu a fannin ilimi.

Ya ce, ta wannan hanya ce jihohi za su iya aiwatar da shirye-shiryen ilimi da suka dace da manufofi da albarkatun da ake da su.

Dakta David ya kara da cewa UNICEF tana bayar da taimakon fasaha wajen shirya wadannan takardu a jihohi takwas.

A cewar NIEPA, UNICEF ta shimfida tubalin shirye-shiryen ilimi bisa hujja, masu daidaito tsakanin jinsi, da fama da nakasassu, tare da karfin jurewa rikice-rikice da sauyin yanayi a Najeriya.

Dakta David ya yaba wa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa jajircewarta wajen sauya tsarin ilimi ta hanyar amfani da bayanai wajen yanke shawara.

 

Shi ma babban  sakatare na ma’aikatar ilimin gaba da sakandare, da fasaha da kimiyya ta jihar, Alhaji Muhammad Dahiru, ya yaba wa abokan hulɗa bisa shawarwarin  da suke bayarwa.

A cewarsa, Gwamnatin Jihar Jigawa tana da cikakken kudiri na yin aiki tare da abokan hulda domin samar da ingancin ilimi a jihar.

Dahiru ya ce daya daga cikin ginshikan gwamnatin Namadi shi ne sauya tsarin ilimi.

Hukumar UNICEF tare da hadin gwiwar Tarayyar Turai (EU), suna tallafa wa Jihar Jigawa wajen nazarin sabon tsarin dabarun ilimin jihar.

Wannan aikin yana gudana ne karkashin shirin hadin gwiwa na UNICEF da EU kan ilimi da karfafa matasa.

 

Usman Mohammed Zaria

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nnamdi Kanu: Masu zanga-zanga sun yi watsi da gargaɗin ’yan sanda
  • Juyin mulki: Ana zargin tsohon gwamnan da ɗaukar nauyin sojojin Najeriya
  • Talauci ne babban maƙiyin ɗan Adam — Atiku
  • Sojojin Najeriya: Rahotanni Dangane Da Juyin Mulki Wa Shugaba Tinubu Ba Gaskiya Bane
  • Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
  • Ta’addanci: An fi kashe Musulmi a kan Kiristoci a Najeriya — Jakadan Amurka
  • NIEPA Ta Jinjinawa UNICEF Bisa Kare Hakkokin Yara Na Samun Ilimi A Najeriya
  • Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya
  • Ba mu ji dadin yi wa mahaifinmu afuwa tare da riƙaƙƙun masu laifi ba – Iyalan Herbert Macaulay