Aminiya:
2025-12-03@22:39:12 GMT

Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan kara aure a Kano

Published: 19th, October 2025 GMT

Wani magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan yadda zai jibinci lamirin hana shi ƙarin aure da matarsa ta yi a Jihar Kano.

Aminiya ta ruwaito cewa magidancin dai ya ziyarci Babban Ofishin ’Yan sanda da ke Bompai domin neman shawara.

Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano Gwamnati ta ɗauki matakin rage shan gishiri a Nijeriya

Kakakin rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya sanar da hakan cikin wani sako da ya wallafa jiya Asabar a shafinsa na Facebook.

A cewar jami’in, mutumin wanda matarsa ta hana shi ƙara aure yana neman a yi masa ƙarin haske kan abin da doka ta tanada game da amfani da kuɗi domin yi wa mai ɗakinsa dannar ƙirji.

SP Kiyawa ya ce magidancin ya je ofishin ne domin neman shawara a kan ko doka ta ba shi damar amfani da kuɗi har naira miliyan biyu wajen shawo kan matarsa dangane da buƙatarsa.

Tuni dai jama’a suka soma bayyana ra’ayoyi kan wannan mas’ala, inda wasu ke ganin hakan ya dace, wasu kuma na ba da shawarar magidancin ya bai wa dangin matar kuɗin.

Wasu ko cewa suke ai wannan wani nau’i ne na cin hanci da rashawa da dai sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno

’Yan sanda sun gano tare da miƙa wa wata mata zinarenta da kuɗinsu ya kai Naira miliyan 23 da suna ɓace a lokacin wani harin Boko Haram shekara 13 da suka gabata a Jihar Borno.

Jami’an tsaro da ke sintiri a kan iyakar Jihar Borno da Nijar ne suka gano kayan zinaren da suka ɓace tuna shakarar 2012, waɗanda suka haɗa da sarƙoƙi da sulallan zinariya a yankin Ƙaramar Hukumar Abadam.

Jami’an Ƙaramar Hukumar ne suka sanar a ranar Asabar a Malam Fatori cewa tsabar zinaren da aka gano, darajarsu ta kai Naira miliyan 23, mallakin wata uwa ce mai ’ya’ya shida.

Matar, wacce ke zaune a gaɓar Tafkin Chadi, ta ce, “A yau ina cike da farin ciki game da gano tsabar zinare na masu daraja da suka ɓace tun 2012, lokacin da ’yan Boko Haram suka ƙona gidaje da shaguna da yawa a cikin al’ummarmu.”

Ta jaddada cewa, “babu daga cikin zinare da aka samu ya ɓace ko ya lalace a lokacin mamayar Malam Fatori da ’yan ta’adda suka yi fiye da nawa.”

Wani babban jami’in Majalisar Ƙaramar Hukumar Abadam da ya sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya yaba wa ’yan sandan da aka tura don kare rayukan mutane da kadarorinsu a yankin Tafkin Chadi.

Bayan gano tsabar zinare na naira miliyan 23, jami’in ya lura cewa martanin ’yan sanda a ayyukan yaƙi da ta’addanci da ake ci gaba da yi wani abin karfafa gwiwa ne ga sojoji da sauran hukumomin tsaro a yankin Tafkin Chadi, wanda ya ƙunshi qananan hukumomi takwas da ke yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi