Aminiya:
2025-10-19@14:18:22 GMT

Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan kara aure a Kano

Published: 19th, October 2025 GMT

Wani magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan yadda zai jibinci lamirin hana shi ƙarin aure da matarsa ta yi a Jihar Kano.

Aminiya ta ruwaito cewa magidancin dai ya ziyarci Babban Ofishin ’Yan sanda da ke Bompai domin neman shawara.

Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano Gwamnati ta ɗauki matakin rage shan gishiri a Nijeriya

Kakakin rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya sanar da hakan cikin wani sako da ya wallafa jiya Asabar a shafinsa na Facebook.

A cewar jami’in, mutumin wanda matarsa ta hana shi ƙara aure yana neman a yi masa ƙarin haske kan abin da doka ta tanada game da amfani da kuɗi domin yi wa mai ɗakinsa dannar ƙirji.

SP Kiyawa ya ce magidancin ya je ofishin ne domin neman shawara a kan ko doka ta ba shi damar amfani da kuɗi har naira miliyan biyu wajen shawo kan matarsa dangane da buƙatarsa.

Tuni dai jama’a suka soma bayyana ra’ayoyi kan wannan mas’ala, inda wasu ke ganin hakan ya dace, wasu kuma na ba da shawarar magidancin ya bai wa dangin matar kuɗin.

Wasu ko cewa suke ai wannan wani nau’i ne na cin hanci da rashawa da dai sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

Maganar mace tana iya gina aure ko rusa shi. Idan kika yi amfani da harshenki wajen zagi, tsinuwa, da cin zarafi, kin riga kin fara gina bango tsakaninki da mijinki. Kuma wannan kuskure ne da ake yin kuka a kai daga baya.

7. Barin kanki ba kula da kanki

Mace da ta daina kula da tsafta, kamshi, da kwalliya a cikin gida tana sa mijinta ya fara daina ganin armashinta, ki kula, mijinki zai iya samun abin da ke burge shi a waje, amma bai kamata ya rasa hakan a wurinki ba. Wannan babban kuskure ne da za ki yi nadama idan kika yi sakaci.

 

8. Rashin zama mai hakuri

Aure ba kyakkyawa ba ne kadai, akwai gwaji, akwai jarabawa. Idan mace ba ta da hakuri, tana iya ruguza gidan aurenta da kanta. Hakuri shi ne kashin bayan nasarar kowanne aure.

 

9. Kin sanin darajar mijin ki

Idan kika daina nuna masa cewa ke kina godiya da shi, kina ganin komai ya zama dole, to kin fara ruguzawa. Miji yana bukatar a yaba masa, a nuna masa daraja. Idan kika yi sakaci, sai ya fara neman inda zai sami hakan.

 

10. Kin guje wa shawarar Allah

Dukkan kuskuren da aka ambata a sama ya samo asali daga barin koyarwar addini. Idan mace ta tsaya da gaskiya, ta kiyaye umarnin Allah da na Manzonsa, ba za ta aikata wadannan kurakurai ba. Amma idan ta bar su, aure na zama cike da nadama da bakin ciki.

 

Karshen magana:

Kuskure a aure na iya zama karami a idon mace, amma yana iya zama babban abu da zai rusa ginin da ta dauki shekaru tana ginawa. Kada ki bari wata rana ki ce “Da na sani.” Saboda lokacin da kalmar nan ta fito, lallai nadama ta riga ta mamaye zuciyarki.

Ki tsaya, ki gyara, ki kasance mace ta daban mace mai daraja a idon mijinta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Uwargida Sarautar Mata Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1) October 12, 2025 Uwargida Sarautar Mata Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro? September 12, 2025 Uwargida Sarautar Mata Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa  July 27, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun tsare ɗan jarida kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano
  • Magidanci na neman shawarar ’yan sanda kan ƙara aure a Kano
  • Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)
  • Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano
  • ‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe
  • Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU
  • Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
  • HOTUNA: Al’ummar Jihar Neja sun yi addu’o’in neman zaman lafiya
  • Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja