HausaTv:
2025-12-03@23:35:52 GMT

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 153

Published: 19th, October 2025 GMT

153-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littana wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Murtadha Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawa, na maulana jalaluddeen Rumi ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.

////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Hassan Al-Mujtaba(a) dan Fatimah diyar manzon All..(s) da muke kawo muku. Mun yi maganar yadda, addinin musulunci ya himmatu da shugabanci, saboda haka ne ya ciki addini da shi kamar yadda ya zo a cikin aya da 3 na suratul Ma’ida.

Sannan mun ji yadda Amirulmumina (a) yayi wasiyya ga dansa Imam Hassan (a) da kuma kaninsa Imam Alhussain (a) a bayansa. Mun bayyana cewa manzon All..(s) tare da umurnin All..ya bayyana cewa khalifofi a bayansa 12 har duniya ta nade na farkonsu Ali(a) sannan yayansa Alhassan da Alhussain daga nan sai yayan Alhussain 9.

Amirul muminina (a) ya yi ishara kan wannan batun a cikin khudubobinsa da dama, inda yake ishara da wadan nan limamai daga iyalan gidan manzon All..(s).

Kamar inda yake cewa {Su ne rayuwar ilmi, da mutuwar jahilci, hakurunsu ne zai sanar da ku ilminsu, da kuma zahirinsu daga badini, yin shirinsu kuma daga hikimar maganasu, basa sabawa gaskiya kuma basa sabani a cikinta, kuma sune ginshakan musulunci, kuma sune mafaka da kuma kariya ga musulmi.

Da su ne gaskiya yake koma inda ya dace da shi, sannan bata yake kaucewa daga inda yake, harshen karye yake yankewa daga tushensa, sun rike addini rikon kareshi da kuma aikata shi, bar ikon ji da sani da kuma fada kawai ba, lalle masu fadar ilmi suna da yawa, amma masu kiyaye ilmin a aikace kadan ne}

Har’ila yau dangane da su manzon All..(s) yana cewa {Wannan addinin ba zai gushe a tsaye kamar yadda yake ba har zuwa ranar kiyama, idan har shuwagabannin 12 ne zasu zama khalifofib, dukkaninsu kuraishawa ne}. A wani hadisi yana ce {Al-Hassan da Alhusain limamai ne sun tashi ko sun zauna}, ma’a sun tashe sun yi yaki ko sun yi sulhu.

Da wasu hadisai da dama dangane da su. Don haka bayan kammala jana’izar Mahaifinsa, da zartar da hukuncin kisasi kan ibnu Muljam, Imam Hassan (a) a ranar 21 ga watan Ramadan ya je masallacin mahaifinsa A kufa, ya hau kann mimbari, sannan sahabban mahaifinsa da wasu sahabban manzon All..(s) da sauran mutanen kufa suka cika masallacin, sannan ya fara khudubarsa ta farko inda yake cewa {Hakika an dauki ran mutum a cikin wannan daren, wanda magaba basu kama kafarsa a ayyuka ba, kuma na baya ba zasu kama kafarsa ba a ayyukan alkhairi, hakika ya kasance yana jihadi tare da manzon All..(S) inda yake kareshi da ransa, manzon All..(s) ya kasance yana aika shi tare da tutarsa, sai mala’ika jibrilu yana kare shi daga damarsa sannan mika’ilu yana kare shi daga hagunsa, ba zai dawo ba sai All…ya yi bashi nasara ta hannunsa.

Hakika yayi wafati a cikin daren da aka dauke Isa dan Maryam(s) (a) daga doron kasa zuwa sama, yayi wafati a daren da Yushau dan nun wasiyin anna musa(a) yayu wafati, bai bar kudade ba sai dirhami 700 wanda ya rage daga cikin albashinsa, yana son ya sayawa iyalansa khidimi da su, ya umurceni da in maida su cikin baitul mali} daga nan ya tuna da mahaifinsa, sai yayi kuka hawaye suka zuba daga idanunsa}.

Daga nan sai dukkan wadanda suke cikin masallacin suka yi kuka da kukansa(a), daga baya sai an yi shi a cikin masallacin, saboda bakin ciki da Rashin Amirul muminina (a), daga nan sai Imam Al-Hassan (a) ya sake tada maganarsa, inda yake cewa

{Ya ku mutane! Wanda ya sanni ya sanni, wanda kuma bai sanni ba, to nine Al-Hassan dan Aliyin, nine dan Annabi (s), nine dan wasiyi, nina dan mai bada Bushara mai gargadi, nine dan mai kira zuwa ga All..da izininsa, nine dan fitila mai haske, ina daga cikin iyalan gida wadanda mala’ika Jibrilu yake sauka yay a tashi daga wajemmu, kuma ina daga cikin Ahlulbaiti wadanda All..ya tafiyar da dauka daga garesu ya tsarkakesu tsarkakewa, kuma ina daga cikin iyalan gidanda All….ya wajabta sonsu a kan duk musulmi, All..mai girma da daukaka ya fadawa annabinsa(s) {Ka ce, Ban tamyeku wata lada a kansa ka, sai so ga dangina na kusa, kuma ga wanda ya aikata mai kyau} kuma aikata mai kyau shi ne sommu Ahlul baiti}

Wannan shi shi khudubar Imam Al-Hassan dan Ali (a) na farko bayan shahadar mahaifinsa Aliyu dan Abitalib (a) kuma ga bayanin wasu daga cikin abubuwan da ya kawo a cikin khudubarsa (s).

Da farko ya bayyanawa mutane matsayin mahaifinsa Imam Ali (a) a musulunci, musamman jihadinsa tare da manzon All..(s), a lokacinda manzon All..(s) yake bashi tuta ya je yaki, ta manya-manyan mala’ikun All..suna tare da shi, kuma sune Jibiru da Mika’il, wannan shi sirrin nasarar da Aliyu dan abitalib ya samu a kan mushirikai a yake yaken da manzon All..(s) yayi a duk tsawon rayuwarsa. Don babu wani yaki wanda manzon All..(s) yayi a rayuwarsa face Aliyu na tare da shi kuma shi ne mai rike da tutar yakin, sai yakin tabuka, wanda ba’a ma yi shi ba.

A manya-manyan yake-yaken wadanda manzon All..(s) ya yi da mushrikai, Aliyu dan Abitalib shi ne kwarzon yakin. A badar shi ya kashe fiye da rabin mushrikan da aka kashe, a uhud bai gudu ba kamar yadda da dama suka gudu, saboda haka ne aka ji masa Rauni kimanik 8 a jikinsa, manzon All..(s) ma an ji masa rauni a wannan yaki. Aliyu shi ne gwarzon yakin Ahzab inda ya kashe amru dan Abduwud, shi ne gwazon Khaibara, inda ya kashe Marhab ya sami nasara a kan yahudawan khaibara. She ne gwarzon Hunain, bai gudu ba, kamar yadda wasu suka gudu, sannan shi yay a kare manzon All..(s) daga mayakan Hunain, ya kuma sami nasara a kansu.

Aliyu(a) ya sami nasarori a dukkan inda manzon All..(s) ya tura shi yaki, yakin zatussalasil, yake yake da dama a Yemen da sauransu.

Sanna a yakin tabuka bai fita da shi ba saboda, akwai makircin da ake son a yiwa addinin musulunci, wanda ya kadai zai iya magance shi.

Har’ila yau ya bayyana yadda mahaifinsa Amirulmuminin (a) yake kare banzan All..da ransa, kama daga daren hijira, inda ya seda ransa ya kwanta a shimfidan manzon All..(s) bayan ya san mushrikan Makka sun yanke shawarar kashe a wannan daren. Sanna a yakin Uhudu, shi da wasu  mutane kadan ne suka kare manzon All..daga mushrikai.

Sannan Imam Al-Hassan (a) ya ca na farko da na karshe basu kama kafarsa a aikin alkhairi ba, don haka wanda ya kasance haka to kuwa shi ne mafi girma da daukaka. Idan ana maganar masu matsayi irinsa a cikin wasiyan annabawa da bayin All..da aka yi ko za’a yisu nan gaba, ba wanda zai kama kafarsa. A hadisi manzon All..(s) yana cewa Aliyu (a) shi ne siddiki mafi girma.

02-Imam ya bayyana darajan daren da mahaifinsa ya koma ga mahalicinsa, wato shi ne daren da aka yi mirazi da Isa dan Maryam (a), har ila yau shi ne darenda wasiyyin annan Musa (a) Yusha’u dan Nun ya bar duniya shi ma. Wasu malaman shi’a suna daukar daren 21 ga watan Ramadan shi ne daren lailatul Kadiri wanda Alkur’ani mai girma yayi maganarsa. Kuma wasu hadisan manzon All..(s) suka suka bayyana cewa daren yana cikin darare 10 na karshen watan.

Don haka a wannan daren mai albarka ne wasiyyin manzon All..(s) ya koma ga Ubangijinsa mai girma da daukaka.

03-ya bayyana zuhudun mahaifinsa Imam Ali (a), gudun duniya ta sa shi ya kaurace mata, don haka bai bai kome da duniya ba, sai dirhami 700 wadanda suka rage daga cikin albashinsa, wadanda kuma da yar ayu zai sayawa iyalansa kuyanga ko bawa wanda zai taimaka masu a ayyukansu na yau da kullum.

Dukiyar al-umma masu yawa suna shiga hannunsa, amma baya karkata zuwa wannan duniyar kamar yadda wasu shuwagabannin a zamaninsa suka karkata zuwa gareta. Yayi haka don yarda da amincewar abinda All..ya yi masa alkawari a lahira. Sannan a lokacinda ya ga zai bar duniya ya umuce shi, wato Al-Hassan (a) ya maidasu cikin kudaden jama’a, wato Baitul Mali.

04-daga karshe Imam Al-Hassan a cikin khudubarsa ta farko bayana shahadar mahaifinsa, ya fadawa mutane, waye shi. Menen matsayinsi a cikin wannan al-umma da musulmi, inda ya bayyana cewa, shi Alhassan dan Ali, dan kuma annabin wannan al-ummar, tunda mahaifiyarsa diyar manzon All…(s), a nan hadisai da dama sun zo daga manzon All..(s) yana cewa Alhassan da Alhusain yayansa ne.

Kuma inda yake cewa All..ya Sanya zurriyar ko wani annabi daga tsutsunsa, amma ya Sanya zurriyyarsa a tsotson Ali(s). Imam Ali (a) kansa, yakan fadi cewa, Alhassan da Alhusain yayan manzon All..ne, sannan sauran yayansa kuma, yayansa ne. Sannan ya bayyana cewa yana daga cikin wadanda mala’ika jibrilu yake sauka ya tashi a gidansu, yana daga cikin wadanda All..ya tsarkakesu daga sabo, kamar yadda ya zo a cikin alkur’ani, kuma yana daga cikin wadanda All..ya wajabta sonsu a cikin alkur’ani mai girma.

Don haka duk wanda ya ji wannan, shi akwai wanda ya shi Daraja da daukaka da cancantar zama shugaba irinsa?. Don haka Imam Alhassan (a) ne yafi cancanta da kuma dacewa da shugabancin Al-ummar kasansa tunda ba wani dan annabi ko jikan annabi da yak e dan doron kasa a lokacin sai shi da kaninsa Al-hussain (a).

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 152 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 151 October 19, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 150 October 19, 2025 Wata Kotun A Murka Ta Haramtawa HKI Kafa Na’urorin Leken Asiri A Wayoyi Masu WattsApp October 19, 2025 Sojojin Najeriya: Rahotanni Dangane Da Juyin Mulki Wa Shugaba Tinubu Ba Gaskiya Bane October 19, 2025 Hamas Ta Gabatar Da Sunayen Kwararrun Da Zasu Gudanar Da Harkokin Gaza October 19, 2025 Doha: Pakistan da Afghanistan sun amince da tsagaita bude wuta a tsakaninsu October 19, 2025 Isra’ila ta ce mashigar Rafah za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai abin da hali ya yi October 19, 2025 Araqchi: Kuduri Mai Lamba 2231 Ya Zo Karshe October 18, 2025 Kasashen Iran, Rasha, Da China Sun Jaddada Rashin Halaccin Dawo Da Tsohon Takunkumi Kan Iran October 18, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: inda yake cewa kama kafarsa bayyana cewa kamar yadda

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu

Majalisar Dattawa ta amince da wani sabon ƙudiri da ke neman a gyara dokar yaƙi da ta’addanci, domin a ɗauki garkuwa da mutane a matsayin babban laifi na ta’addanci.

Ƙudirin, wanda Sanata Opeyemi Bamidele ya gabatar, ya tanadi hukuncin kisa ga duk wanda aka kama da laifin satar mutane, ba tare da wata zaɓin tara ba.

Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja

Sanata Bamidele, ya ce ƙudirin ya yi daidai da yunƙurin gwamnati da majalisa na kawo ƙarshen matsalar tsaro a ƙasar nan.

Yayin gabatar da ƙudirin, ya ce garkuwa da mutane na ƙara yawaita, kuma ƙungiyoyin miyagu na amfani da shi wajen tara k6udi, abin da ke jefa jama’a cikin tsoro da kuma daƙile karatun yara a jihohi da dama.

Sanatoci da dama sun goyi bayan hukuncin kisa, inda suka bayyana cewa hakan zai zama gargaɗi ga masu aikata wannan mummunan laifi.

Wasu kuma sun nemi a hukunta bankunan da ke taimakawa wajen aikewa ko karɓar kuɗaɗen fansa, yayin da wasu suka ce ya kamata a daina yi wa ’yan ta’adda afuwa.

Majalisar ta tura ƙudirin zuwa kwamitoci na musamman domin bincike, tare da umarnin su kawo rahoto cikin makonni biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta
  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%