Nnamdi Kanu: Masu zanga-zanga sun yi watsi da gargaɗin ’yan sanda
Published: 20th, October 2025 GMT
’Yan sanda da jami’an tsaron farin kaya (DSS) sun shiga shirin ko-ta-kwana a birnin Abuja bayan masu zanga-zangar neman a saki shugaban ’yan awaren Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu, sun yi watsi haramcin kotu kan yin hakan a kusa da Fadar Shugaban Ƙasa.
An shirya zanga-zangar ce ƙarƙashin jagorancin tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa kuma mai fafutukar #RevolutionNow, Omoyele Sowore, domin matsa wa gwamnati lamba ta saki Kanu, wanda ke tsare tun shekarar 2021, kan zargin ta’addanci da cin amanar ƙasa.
Shaidu sun bayyana cewa an fara sanya shingayen bincike a wasu manyan hanyoyi da ke kaiwa Majalisar Dokoki ta Ƙasa, hedkwatar rundunar ’yan sanda, dandalin Eagle Square da Kotun Ɗaukaka Ƙara tun ranar Lahadi.
Nnamdi Kanu, wanda ke fuskantar tuhumar ta’addanci da cin amanar ƙasa, an fara kama shi a 2015, aka ba shi beli a 2017, kafin ya tsere bayan harin da sojoji suka kai gidansa a Abia.
Juyin mulki: Ana zargin tsohon gwamnan da ɗaukar nauyin sojojin Najeriya NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?Duk da cewa kotuna da dama sun bayar da umarnin a sake shi, Gwamnatin Tarayya ta ƙi bin hukuncin, abin da ke haifar da ƙarin fushi da nuna rashin jin daɗi daga jama’a.
Da yake jawabi kafin zanga-zangar, Sowore ya ce za su ci gaba da tafiyar da shirin kamar yadda aka tsara, yana mai jaddada cewa ’yan Najeriya na da cikakken ’yancin yin zanga-zanga cikin lumana.
“Tsare Nnamdi Kanu ba bisa doka ba ne, kuma abin kunya ne ga ƙasa,” in ji Sowore. “Kotun Ɗaukaka Ƙara ta wanke shi tun 2022, amma gwamnati ta ƙi bin hukuncin.”
Ya kuma roƙi sabon Kwamishinan ’Yan Sanda na Abuja da kada ya yi amfani da ƙarfi wajen tarwatsa masu zanga-zangar.
“Duk wani jami’i da ya ci zarafin masu zanga-zanga za a ɗauki mataki a kansa. Lokaci ya wuce da ake danniya da take haƙƙin jama’a,” in ji Sowore.
Sai dai Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, ya umurci jami’ansa su tabbatar da bin umarnin kotun tarayya da ta hana gudanar da zanga-zanga a kusa da Fadar Shugaban Ƙasa da wasu wurare masu muhimmanci a Abuja.
“Rundunar ’yan sanda za ta ci gaba da tabbatar da doka da oda bisa tsarin mulki,” in ji mai magana da yawun rundunar, Benjamin Hundeyin.
“Duk wanda ya karya doka ko ya tayar da hankalin jama’a za a kama shi kuma a gurfanar da shi.”
A cewar ’yan sanda, matakin na nufin kare tsaron ƙasa da hana tashin hankali a muhimman wuraren gwamnati.
A nasa bangaren, masanin harkokin tsaro kuma shugaban cibiyar RULAAC, Mista Okechukwu Nwanguma, ya gargaɗi gwamnati da ta guji amfani da ƙarfi wajen murƙushe masu fafutuka, yana cewa hakan na iya tayar da ƙarin fitina.
“Kungiyar IPOB ta samo asali ne daga jin an ware su da rashin adalci,” in ji shi. “Idan gwamnati ta saki Kanu ta hanyar tattaunawa da bin doka, hakan zai taimaka wajen kawo zaman lafiya a kudu maso gabas.”
Ya kuma bukaci gwamnati ta rage amfani da ƙarfin sojoji a yankin, ta ƙarfafa ’yan sanda na al’umma, tare da magance matsalolin rashin aiki, talauci da jin wariya.
A cewarsa, lamarin Nnamdi Kanu gwaji ne ga gwamnatin Najeriya wajen tabbatar da adalci, hadin kai da mutunta dokar ƙasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20
Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Shugaban Amurka Donald Trump na cire Pretoria daga taron G20 na shekara mai zuwa, yana mai sake tabbatar da matsayin Afirka ta Kudu na memba da aka kafa wannan dandali na kasa da kasa tare da ita.
Trump ya sanar a ranar Laraba da ta gabata cewa ba za a gayyaci Afirka ta Kudu zuwa taron G20 na 2026 a Florida ba, yana mai ambaton zargin da ake yi wa kasar na kin mika shugabancin G20 ga wakilin ofishin jakadancin Amurka a bikin rufe taron da aka yi a kasar a baya. Duk da haka, Pretoria ta dage cewa shugabancin da ake yi nak aba-karba an mika shi ga wani jami’in Amurka.
Bayan kauracewa taron shugabannin G20 da aka gudanar a Johannesburg a ranar 22-23 ga Nuwamba a karkashin shugabancin Afirka ta Kudu, Trump ya maimaita ikirarinsa na cewa gwamnatin kasar mai rinjayen bakaken fata tana nuna wariya ga tsirarun fararen fata.
A jawabinsa, Ramaphosa ya kira zarge-zargen Trump na kisan kare dangi da kwace filaye daga fararen fata da cewa ba gaskiya ba ne, zargui ne maras hujja balantana makama, yana mai sake jaddada cewa “Afirka ta Kudu cikakkiyar memba ce da aka kafa G20 tare da ita.”
Rikicin da ke tsakanin Washington da Pretoria ya fara kamari ne a farkon 2025. A ranar 14 ga Maris, Amurka ta kori jakadan Afirka ta Kudu, Ebrahim Rasool, bayan ya zargi Shugaban Amurka Donald Trump da abokansa da haɓaka ajandar duniya ta masu ra’ayin wariyar launin fata
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165 December 1, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164 December 1, 2025 Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya December 1, 2025 Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3 A Kasar Lebanon December 1, 2025 Kamaru: Madugun Adawa Ya Rasu A Gidan Kaso December 1, 2025 Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi December 1, 2025 Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100% December 1, 2025 Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta December 1, 2025 Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta December 1, 2025 Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci