Iran ba ta jiran izinin kowa kan tace uranium, Dole ne Amurka ta daina maganar banza_Jagora
Published: 21st, May 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce iran ba ta bukatar izinin kowa kan inganta sinadarin urenium din ta, don haka Amurka ta daina maganar banza da dagewa akan wannan batu inji shi.
Ayatullah Khamenei ya kara da cewa, babban kuskure ne a ce su (Amurka) ba za su bari Iran ta inganta sinadarin Uranium ba.
Ayatullah Khamenei ya bayyana shakkunsa game da sakamakon tattaunawar da ake yi tsakanin Iran da Amurka.
Jagoran ya bayyana hakan ne a yayin bikin tunawa da zagayowar ranar shahadar tsohon shugaban kasar Ibrahim Raisi.
A lokacin mulkin shahid Raisi, an gudanar da shawarwari irin haka da Amurka, amma ba a kai ga cimma wani sakamako ba, inji shi, Don haka, ba ma fatan wani sakamako daga wadannan shawarwarin, kuma ba mu san abin da zai biyo baya ba.”
Ayatullah Khamenei ya yaba da irin tsayin dakan da Raisi ya yi, yana mai jaddada cewa bai taba barin makiya su iya tilastawa Iran zama kan teburin tattaunawa ta hanyar barazana, matsin lamba ko yaudara ba.
Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya kuma yi karin haske dangane da dagewar da Amurka da sauran kasashe suka yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta inganta sinadarin Uranium ba.
“Tabbas, zan bayyana wa al’ummar Iran daga baya dalilin da ya sa suka dage kan batun inganta sinadarin Uranium.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: inganta sinadarin Khamenei ya
এছাড়াও পড়ুন:
Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
Shugaban aksar Iran, Massoud Pezeshkian, ya bayyana cewa martanin sojojin kasarsa ga Isra’ila zai zama mafi muni idan hare-haren Isra’ilar suka ci gaba.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da firaministan Pakistan Shehbaz Sharif, shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa dakarun gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran za su dauki kwararan matakan mayar da martani mai tsauri idan har gwamnatin Isra’ila ta ci gaba da kai farmaki kan Iran.
“Masu da’awar kare hakkin bil’adama ba wai kawai suna goyon bayan zaluncin gwamnatin sahyoniyawa ba ne, har ma suna karfafa mata gwiwar aikata wadannan munanan ayyuka ta hanyar ba ta makamai da kayan aiki,” in ji shi.
Mr. Pezeshkian ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila da ke samun goyon bayan Amurka da kasashen yammacin Turai ta sabawa dukkanin dokokin kasa da kasa.
A nasa bangaren, firaministan Pakistan ya bayyana goyon bayan kasarsa ga al’ummar iran, yana mai yin Allah wadai da keta hurumin kasar Iran da ‘yancinta, wanda ya zama cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD.
Sharif ya sake jaddada cewa Iran na da cikakken ‘yancin kare kanta a karkashin doka ta 51 na kundin tsarin mulkin MDD inda ya bayyana fatan ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.